Sin Na Fatan Dukkan Bangarori Za Su Guji Daukar Mataki Da Zai Ta’azzara Rikici A Gaza
Published: 19th, March 2025 GMT
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta bayyana a yayin da take mayar da martani ga tambayar da wani dan jarida ya yi mata a taron manema labaru na yau 18 ga wata cewa, kasar Sin ta damu matuka kan halin da ake ciki a tsakanin Falasdinu da Isra’ila,kuma tana fatan dukkan bangarorin za su sa kaimi ga ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta yadda ya kamata, da kaucewa daukar duk wani mataki da zai ta’azzara lamarin, da hana afkuwar bala’in jin kai a mataki mai girma.
Hukumomin lafiya da ke Gaza sun ce adadin mutanen da suka mutu a hare-haren da Isra’ila ta kai a wurare daban-daban a zirin Gaza da safiyar Talata ya kai 412. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
Shugaban kasar Iran Masud pezeshkiyan a wajen taron zaman lafiya na turkmanistan ya bayyana cewa siyasar kasashe masu karfin fada aji a yammacin Asiya ne suka bawa isra’ila wata dama ta musamman ta kai hare-hare gaba gadi, da hakan ya bata damar kai harin soji kan kasashen yankin ciki har da kasar iran ba tare da fuskantar wani sakamako ba.
Har ila yau shugaba peszeshkiyan da yake bayani a wajen taron zaman lafiya a garin Ashgabat na kasar Turkministan ya kara da cewa harin da Isra’ila ta kai wa iran a watan yuni da ya kai ga shahadar mutane da dama da basu san hawa ba balle sauka ya samu kyakkawar tarba ne ma mai makon yin Allah wadai
Yace babu wani mataki na ladabtarwa da aka dauka ga wadda ta kai harin , ta ma samu cikakkiyar goyon bayan siyasa da soji ne daga kasahen masu ikirarin kare hakkin bil adama da kuma samar da zaman lafiya, matukar aka ci gaba da bada irin wannan dama ta musamman to babu wanda zai iya yin Magana kan zaman lafiya ko kuma wani umarni na kasa da kasa.
Daga karshe shugaba pezeshkiyan ya godewa Turkmenistan da ta dauki nauyin shirya wannan taro wanda ya zo dadai da aka cika shekaru 30 da amincewa da zama yar baruwanmu a wannan kasa, kana kuma yayi kiran cewa suna goyon bayan duk wani shiri na karfafa tunani kan zaman lafiya da tsaro da ci gaban dan adam da na dabi’a .
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan December 12, 2025 Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa December 12, 2025 Duniyarmu A Yau: Iran Da Kokarin Juyin Mulkin Amurka A Yakin Kwanaki 12, Wa Ya Sami Nasara? December 12, 2025 Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai December 12, 2025 Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin December 12, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut December 12, 2025 Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba December 12, 2025 Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026 December 12, 2025 Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza December 12, 2025 Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci