Leadership News Hausa:
2025-10-25@17:42:42 GMT

Waiwaye: Jihohin Da Aka Taɓa Sanya Dokar Ta-ɓaci A Nijeriya

Published: 19th, March 2025 GMT

Waiwaye: Jihohin Da Aka Taɓa Sanya Dokar Ta-ɓaci A Nijeriya

Dalilin wannan doka shi ne rikice-rikicen addini tsakanin Musulmai da Kiristoci a watan Satumba 2001, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 2,000.

 

A Jihar Borno Ma An Taɓa Sanya Dokar, Amma Ba A Jihar Baki Ɗaya Ba

 

A shekarar 2011, Shugaba Goodluck Jonathan ya ayyana dokar ta-ɓaci a wasu ƙananan hukumomin jihohin Borno, Adamawa, da Yobe saboda yawaitar hare-haren Boko Haram.

 

A 2013, Jonathan ya faɗaɗa dokar ta-ɓacin zuwa ɗaukacin jihohin Borno, Yobe, da Adamawa sakamakon tsanantar matsalar tsaro.

 

Wannan mataki ya bai wa jami’an tsaro ƙarin iko domin dawo da zaman lafiya.

 

Sai Kuma Jihar Ribas a Yanzu

 

Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas saboda rikicin shugabanci da matsalolin tafiyar da gwamnati.

 

Shugaban Ƙasa Yana Da Dama Bisa Doka

 

Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999 ya bai wa Shugaban Ƙasa damar ayyana dokar ta-ɓaci a wata jiha idan ana fuskantar matsalar tsaro ko rikicin shugabanci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: dokar ta ɓaci a

এছাড়াও পড়ুন:

Tun da PDP ta bar mulkin Najeriya maguɗin zaɓe ya ragu – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce tsarin zabe a Najeriya ya samu gagarumin ci gaba tun bayan da jam’iyyar PDP ta bar mulkin kasar a matakin tarayya.

Akpabio, wanda aka zabe shi sau biyu a matsayin gwamna karkashin PDP kuma ya fara shiga majalisar dattawa a karkashin jam’iyyar, ya bayyana hakan ne a lokacin karatu na biyu a kan dokar gyaran tsarin zabe a zaman majalisa da aka yi a ranar Laraba.

Dangote zai sayar da kaso 10 na hannun jarin matatar man shi NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Haraji Da Zai Fara Aiki A 2026

“Ina da tabbacin cewa ni da Sanata Abaribe, wanda muka shafe kusan shekaru 25 muna cikin harkar siyasa, na san ba mu damu da jam’iyya ba, ana iya lashe zabe a ko’ina.

“Ka na da ƙwarewa sosai, amma za ka yarda da ni cewa tun bayan faduwar PDP, zabe ya inganta matuka a wannan ƙasa.

“Na tuna, ina da kusanci da yawancin shugabannin ƙasa tun daga 1999, kuma a 2007 lokacin da na ci zabe a matsayin gwamna, shugaban ƙasa na lokacin, Allah ya jiƙansa, Shugaba Yar’Adua, ya fito fili ya ce zaben da ya kawo shi mulki yana da lam’a.

“Ya ce cike yake da kura-kurai da magudi. Tun daga lokacin, muka fara rufe guraben da ke haifar da matsala.”

Akpabio ya ƙara da cewa duk da cewa ’yan Najeriya na fuskantar ƙalubale, tsarin ya inganta.

“Ka duba zaben da ya gabata, har sai da muka je Kotun Koli muna muhawara kan ko lashe babban birnin tarayya kadai ya isa ya sa dan takara ya zama shugaban ƙasa,” in ji shi.

“Hankali kawai ya isa ya gaya mana cewa ba haka dokar zabe take nufi ba,” in ji Akpabio.

Shugaban majalisar dattawa ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki bayan PDP ta fadi zabe a shekarar 2015.

Ya tsaya takarar Sanata a 2019 a karkashin jam’iyyar APC, amma bai ci ba.

Sai dai tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya naɗa shi minista daga bisani, kafin a 2023 kuma ya ci zaben sanatan daga jiharsa ta Akwa Ibom, sannan aka zabe shi shugabancin majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sauke Hafsoshin Tsaro: Za a yi wa Janar-Janar 60 ritaya daga aiki
  • Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
  • Tinubu ya faɗa wa ’yan Najeriya dalilin sauya hafsoshin tsaro — ADC
  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci
  • Tinubu ya sauke hafsoshin tsaro, ya maye gurbinsu da wasu
  • Majalisar Tattalin Arziki Ta Amince da Shirin Gyara Cibiyoyin Horar da Jami’an Tsaro
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno
  • Boko Haram sun kai sabbin hare-hare a wasu yankunan Borno da Yobe
  • Tun da PDP ta bar mulkin Najeriya maguɗin zaɓe ya ragu – Akpabio
  • ISWAP: Mun kawar da duk wata barazana — Gwamnatin Ondo