Leadership News Hausa:
2025-11-25@02:09:38 GMT

Waiwaye: Jihohin Da Aka Taɓa Sanya Dokar Ta-ɓaci A Nijeriya

Published: 19th, March 2025 GMT

Waiwaye: Jihohin Da Aka Taɓa Sanya Dokar Ta-ɓaci A Nijeriya

Dalilin wannan doka shi ne rikice-rikicen addini tsakanin Musulmai da Kiristoci a watan Satumba 2001, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 2,000.

 

A Jihar Borno Ma An Taɓa Sanya Dokar, Amma Ba A Jihar Baki Ɗaya Ba

 

A shekarar 2011, Shugaba Goodluck Jonathan ya ayyana dokar ta-ɓaci a wasu ƙananan hukumomin jihohin Borno, Adamawa, da Yobe saboda yawaitar hare-haren Boko Haram.

 

A 2013, Jonathan ya faɗaɗa dokar ta-ɓacin zuwa ɗaukacin jihohin Borno, Yobe, da Adamawa sakamakon tsanantar matsalar tsaro.

 

Wannan mataki ya bai wa jami’an tsaro ƙarin iko domin dawo da zaman lafiya.

 

Sai Kuma Jihar Ribas a Yanzu

 

Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas saboda rikicin shugabanci da matsalolin tafiyar da gwamnati.

 

Shugaban Ƙasa Yana Da Dama Bisa Doka

 

Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999 ya bai wa Shugaban Ƙasa damar ayyana dokar ta-ɓaci a wata jiha idan ana fuskantar matsalar tsaro ko rikicin shugabanci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: dokar ta ɓaci a

এছাড়াও পড়ুন:

Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno

Mayaƙan Boko Haram masu biyayya ga Ali Ngulde sun fille kan mata biyu a yankin Dutsen Mandara da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza a Jihar Borno.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa mayaƙan sunyi wa matan kisan gilla ne bisa zargim yin shirka.  

Ƙungiyar ta kama matan ne da layu a lokacin bincike, inda a bidiyo da suka fitar, mayakan suka ce hakan shaida ce ta bin hanyar da suka kira haramtacciya.

An kai matan zuwa tsaunuka, aka aiwatar da hukunci a bainar jama’a domin tsoratar da mutane da kuma tilasta bin koyarwar ƙungiyar.

Rahotanni sun nuna cewa ɓangaren Ali Ngulde ya ƙara tsaurara matakan hukunci a ’yan watannin nan, inda ake kai hare-hare kan mutanen da ake zargi da sihiri, leƙen asiri, ko kuma yunkurin tserewa.

Sace ɗalibai: Idan ba zai iya ba ya sauka kawai— PDP Umarnin janye ’yan sanda daga faɗin manyan mutane na iya zama magana kawai —Shehu Sani

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro
  • Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno
  • Boko Haram ta file kan mata 2 a Borno
  • Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana
  • Najeriya: Kungiyar Yan Ta’adda Ta ISWAP Ta Sace Yan Mata 13 A Jihar Borno
  • Tinubu Ya Janye ‘Yan Sanda Daga Tsaron Manyan Mutane, Ya Amince Da Daukar Sabbin 30,000
  • ISWAP ta sace ’yan mata 13 a Borno
  • Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 
  • Ribadu Ya Gana da Sakataren Yakin Amurka Kan Batun Kashe Kiristoci A Nijeriya
  • Obi ya yi watsi da hukuncin ɗaurin rai da rai da aka yi wa Kanu