Waiwaye: Jihohin Da Aka Taɓa Sanya Dokar Ta-ɓaci A Nijeriya
Published: 19th, March 2025 GMT
Dalilin wannan doka shi ne rikice-rikicen addini tsakanin Musulmai da Kiristoci a watan Satumba 2001, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 2,000.
A Jihar Borno Ma An Taɓa Sanya Dokar, Amma Ba A Jihar Baki Ɗaya Ba
A shekarar 2011, Shugaba Goodluck Jonathan ya ayyana dokar ta-ɓaci a wasu ƙananan hukumomin jihohin Borno, Adamawa, da Yobe saboda yawaitar hare-haren Boko Haram.
A 2013, Jonathan ya faɗaɗa dokar ta-ɓacin zuwa ɗaukacin jihohin Borno, Yobe, da Adamawa sakamakon tsanantar matsalar tsaro.
Wannan mataki ya bai wa jami’an tsaro ƙarin iko domin dawo da zaman lafiya.
Sai Kuma Jihar Ribas a Yanzu
Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas saboda rikicin shugabanci da matsalolin tafiyar da gwamnati.
Shugaban Ƙasa Yana Da Dama Bisa Doka
Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999 ya bai wa Shugaban Ƙasa damar ayyana dokar ta-ɓaci a wata jiha idan ana fuskantar matsalar tsaro ko rikicin shugabanci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: dokar ta ɓaci a
এছাড়াও পড়ুন:
Mayaƙan ISWAP sun sace Janar sun kashe sojoji a Borno
Rahotanni na nuni da cewa mayaƙan ƙungiyar ISWAP sun yi garkuwa da wani Janar ɗin sojan Najeriya tare da kashe sojoji da dama a wata Arangama a Jihar Borno.
Ayaraijn motocin sojojin ya faɗa a harin kwanton ɓaunan mayaƙan ISWAP ne a daren Juma’a a Jihar Borno.
Rahotanni na nuna cewa mayaƙan sun yi garkuwa da Janar ɗin tare da hallaka sojoji da dama da ke tare da shi, ciki har da mambobin CJTF.
Rahoton kafar HumAngle — cibiyar da ke mayar da hankali kan rikice-rikice da batutuwan jin ƙai — wanda PremiumTimes ta ruwaito, ya ce Janar ɗin da aka yi garkuwa da shi shi ne kwamandan wani bitget ɗin soji, kuma shi ne yake jagorantar dakarun a lokacin.
Idan ta tabbata, “wannan shi ne karo na farko da wata ƙungiyar ta taɓa kama wani Janar da ke kan aiki a fagen daga,” a cewar HumAngle.
Duk da cewa ’yan ta’adda sun kashe manyan jami’an soja a wasu hare-hare, amma ba kasafai ake samun labarin garkuwa da jami’an soja masu muƙami irin wannan ba.
Har yanzu hukumomin soji ba su fitar da sanarwa kan lamarin ba, kuma ba a tabbatar da adadin waɗanda suka mutu ba.
Kakakin Rundunar Sojin Najeriya, Laftanar-Kanar Onyechi Anele, bai amsa sakon tambaya da aka tura masa kan lamarin ba.
HumAngle ta ce tana bibiyar al’amuran, kuma za ta ci gaba da kawo sabon bayani idan ya samu.