Waiwaye: Jihohin Da Aka Taɓa Sanya Dokar Ta-ɓaci A Nijeriya
Published: 19th, March 2025 GMT
Dalilin wannan doka shi ne rikice-rikicen addini tsakanin Musulmai da Kiristoci a watan Satumba 2001, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 2,000.
A Jihar Borno Ma An Taɓa Sanya Dokar, Amma Ba A Jihar Baki Ɗaya Ba
A shekarar 2011, Shugaba Goodluck Jonathan ya ayyana dokar ta-ɓaci a wasu ƙananan hukumomin jihohin Borno, Adamawa, da Yobe saboda yawaitar hare-haren Boko Haram.
A 2013, Jonathan ya faɗaɗa dokar ta-ɓacin zuwa ɗaukacin jihohin Borno, Yobe, da Adamawa sakamakon tsanantar matsalar tsaro.
Wannan mataki ya bai wa jami’an tsaro ƙarin iko domin dawo da zaman lafiya.
Sai Kuma Jihar Ribas a Yanzu
Shugaba Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas saboda rikicin shugabanci da matsalolin tafiyar da gwamnati.
Shugaban Ƙasa Yana Da Dama Bisa Doka
Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya na 1999 ya bai wa Shugaban Ƙasa damar ayyana dokar ta-ɓaci a wata jiha idan ana fuskantar matsalar tsaro ko rikicin shugabanci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: dokar ta ɓaci a
এছাড়াও পড়ুন:
Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko
Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Rano, A Jihar Kano:
Haduwa da kawayen banza da kuma kuntatawa da wasu malaman suke nuna musu, saboda kin amincewa da su na bukatun da suke nema a wajensu. Da yawa iyayen ba sa tsayawa su saurari matsalolin ‘ya’yansu kan abin da ke damunsu a makaranta, da kuma rashin bibiyar karatunsu da abokansu. Iyaye su tabbatar da suna bawa yara kudi da kayan abincin da zai ishesu idan a makarantun kwana suke, sannan su tabbatar da tarbiyyar malaman da za su kai yaran nasu.
Sunana Aisha Isah Gama (Mai Waka), Jihar Kano:
A gaskiya abin da ke janyo wa baya wuce gurba tattun abokai, har da lefin malamai saboda malami ne za ka ga ya kulla soyayya da daliba, kin ga matsala ta farko kenan, sai mu’amala da kawaye marasa tarbiyya, za ki ga baki ragi ‘yar ki da komai ba, amma kawaye sun bata ta. Shawara iyaye mu kula da ‘ya’yanmu, mu ja su a jiki su zama abokan mu, mu rika tunawa kiwo Allah ya ba mu kuma zai tsayar damu ya yi mana tambaya akan kiwon da ya bamu, mu raba su da kawaye.
Sunana Hauwa Abubakar Sarki, daga Suleja, Jihar Neja:
Sautari malamai su ne silar lalacewar dalibai akowane makaranta, daga na islamiyar har na bokon. Ka ga malami ya rasa wacce zai yi soyayya da ita sai dalibar sa, duk da ba haramun bane, amma ba sa bin hanyar da ya dace wajan neman soyayyar daliban nasu. Malamai su ne silar lalacewar wasu daga cikin dalibai, daga lokacin da malami ya nuna kwadayi akan abin hannun dalibar sa walau surar da Allah yayi mata ko kuma abun hannuta (kudi) babu magnar tarbiyya a nan wajan. Sautari babu kyau, saboda duk inda aka ce malami to fa matsayin uba yake ga dalibansa. Su ma kuma dalibai su kasance masu kamu kai da nuna kyakkyawan tarbiyya a duk inda suke.
Sunana Hafsat Sa’eed:
Sai dai in ba tarbiyya suka samu tun farko ba,idan har sun samu tarbiyya, kuma an magance musu matsalolin da ba za su ga wani abu su yi sha’awa ba, ba na tunanin yaro zai lalace. Amma rashin hakan yaro na iya shiga cikin wani yanayi. Wasu kuma akwai tarbiyyar amma sakamakon haduwa da kawaye sai su canja, domin kawa tana iya canja kawa a lokaci daya. Amma akwai wadanda jarrabawa ce, idan Allah ya jarabce ka babu yadda za ka yi sai ka karba ka yi ta addu’a.
Sunana Muktari Sabo Jahun A Jihar Jigawa:
Na farko dai akwai matsalar Tarbiyya wadda ita ce tushen komai, sannan kuma da rashin gata ga wasu, wasu kuma neman abin duniya ne yake kai su ga lalacewa. Munanan abokai kan iya bata abokansu, haka kuma rashin bibiyar iyaye akan lamarin ‘ya’yansu har sai sun fada wani hali. Iyaye su sa hankali da lura akan yaransu, kuma su dage da yi musu addu’a, kuma su san su waye abokan ‘ya’yansu.
Sunana Fatima Nura kila, Jihar Jigawa:
Abin da yake janyo wa mafiya yawa shi ne, san zuciya, kusan shi ne kaso 70% na lalacewar dalibai mata a makarantu. Yana faruwa ne mata sun dau karya sun dorawa rayuwarsu, wata iyayenta rufin asiri gare su, za ta ce sai ta yi abin da kawarta ta yi, bayan samun iyayen kowanne daban. Shawarar ita ce, a kodayaushe mu mata mu daina kallan saman mu, a kodayaushe mu rika kallon kasan mu, hakan shi ne zai sa mana wadatar zuci.
Sunana Hassana Sulaiman, Hadejia, A Jihar Jigawa:
Daga cikin abin da ke kawo lalacewar dalibai musamman ma mata a makarantun boko da kuma islamiyya cikin al’umma, wani lokacin rashin sanin su kansu ne da iyayen basu fiya duba da lamuran yaran nasu matan ba. Dalilin lalacewar wasu daga cikin dalibai a wannan lokacin bai huce na kawaye ba. Saboda kawaye suna taka muhimmiyar rawa wani lokacin fiye ma da iyayensu. Ya kamata iyaye musamman mata, su zama kawaye ga ‘ya’yan nasu dan ta haka ne ‘ya’yan nasu matan za su iya sakin jiki da su suna zaman fira tare a hakan iyayen za su fahimci su waye ne ma yaransu, kuma wani abu ne a ransu wanda za su iya basu shawarar yadda za a magance matsalar maimakon lalacewar su ta sanadiyyar kawaye.
Sunana Hassana Yahaya Iyayi, Jihar Kano:
Yawanci soyayya da malamai ke yi da dalibai shi yake jawo wa. Kin ga kawaye sune kan gaba wajen canja wa yara dalibai tarbiyya da kuma ita soyayyar da malaman ke shinfidawa da yaran. Iyaye dai su rika kulawa da tarbiyyar ‘ya’yansu dan kuwa amana ce Allah ya dora a hannunsu.
Sunana Nabila Dikko, Argungu, Jihar Kebbi:
Lalacewar ɗalibai mata na yawaita ne saboda rashin kulawar iyaye, rinjayar abokai marasa tarbiyya da amfani da kafafen sada zumunta ba tare da iyaka ba. Wasu suna da kamun kai saboda tarbiyyar gida, wasu kuma babu. Shawara, iyaye su kula da ‘ya’yansu, dalibai kuma su tsare mutuncinsu, su mayar da hankali ga karatu.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA