Cire Gwamna Fubara ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki — Lauyoyi
Published: 19th, March 2025 GMT
Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA) ta soki matakin da Shugaba Bola Tinubu ya ɗauka na ayyana dokar ta ɓaci da kuma cire Gwamna Similanayi Fubara na Jihar Ribas.
Cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, shugaban NBA, Mazi Afam Osigwe (SAN), ya ce a ƙarƙashin Kundin Tsarin Mulki, shugaban ƙasar ba shi da ikon tsige zaɓaɓɓen gwamna bayan ayyana dokar-ta ɓaci a jiharsa.
“Saboda haka duk wani matakin da ya saɓa wa tsarin mulkin dimokuraɗiyya wanda kuma ya keta haddin cin gashin kan gwamnatocin jihohi,” in ji shi.
A kan haka ne Ƙungiyar Lauyoyin ta buƙaci Majalisar Dokoki ta Ƙasa da ta yi watsi da duk wani yunƙuri na tsige Gwamnan Jihar Ribas da sauran zaɓaɓɓun jami’an da aka yi ba bisa ka’ida ba.
“Dole ne ya zamanto ayyana da dokar ta ɓaci ta dogara da ƙwararan dalilai na tsarin mulki, ba wai wata manufa ta siyasa ba.”
NBA ta yi gargaɗin cewa akwai barazana mai hatsarin gaske ta dakatar da zaɓaɓɓun jami’an da ke ƙarƙashin dokar ta ɓaci, wanda zai iya kawo wa dimokuraɗiyya cikas na buɗe ƙofar tsige zaɓaɓɓun gwamnatoci a nan gaba.
Kungiyar ta yi kiran cewa duk wani mataki da aka ɗauka a Jihar Ribas ya bi ka’idojin tsarin mulki da kuma ka’idojin dimokuraɗiyyar Nijeriya.
Kazalika, ta buƙaci duk masu ruwa da tsaki da suka haɗa da ɓangaren shari’a, da ƙungiyoyin farar hula, da ƙasashen duniya da su sanya ido sosai kan halin da ake ciki a Jihar Ribas domin daƙile duk wani yunƙuri da ke yi wa masu riƙe da madafun iko katsalandan ba bisa ka’ida ba.
Aminiya ta ruwaito cewa Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas bayan rikita-rikitar siyasa da jihar ta daɗe tana fama da shi tare da kuma da naɗa wanda zai riƙe muƙamin gwamnan jihar na tsawon wata shida.
Tinubu ya sanar da matakin ne a wani jawabi da ya yi ta kafafen talabijin na ƙasar da yammacin ranar Talata.
A cikin jawabin nasa, Tinubu ya yi nuni da yadda aka rushe ginin majalisar dokokin jihar watanni 18 da suka gabata, wadda aka kasa sake gina ta har zuwa wannan lokaci.
“Jihar ta tsaya cik tun bayan ɓarkewar rikicin siyasar inda aka tauye wa al’ummar jihar hakkinsu na cin moriyar mulkin dimokuraɗiyya.
“Na yi iyakar bakin kokarina wajen ganin yadda za a magance matsalar to amma duka ɓangarorin sun yi watsi da yunkurin.”
Tinubu ya ce “Bayan nazari kan halin da ake ciki a Jihar Ribas, ya zama wajibi na yi amfani da sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999.
“A kan haka, na ayyana dokar ta-ɓaci daga yau 18 ga watan Maris, 2025.
“Da wannan bayani, gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu da kuma dukkanin zaɓaɓbun ’yan majalisar dokokin Jihar Ribas, an dakatar da su na wata shida, a matakin farko.
“A halin yanzu, na naɗa Vice Admiran Ibokette Ibas a matsayin wanda zai gudanar da lamurran jihar, domin amfanin al’ummar jihar,” in ji Tinubu.
Sai dai a cikin jawabin nasa, Tinubu ya bayyana cewa wannan doka da ya ƙaƙaba ba ta shafi ɓangaren shari’a na jihar ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Ta Ɓaci Jihar Ribas Ƙungiyar Lauyoyi Siminalayi Fubara a Jihar Ribas
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Abba ya gabatar da kasafin 2026 na N1.36trn
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gabatar da kasafin 2026 na kuɗi Naira tiriliyan 1.36 tiriliyan a Majalisar Dokokin jihar.
Kasafin wanda aka yi laƙabi da “Kasafin Gine-gine, Ci Gaban Kowa da Ɗorewar Ci Gaba.”
Dukiyar sama da miliyan 500 ta kone a gobarar kasuwar katako ta Gombe Tinubu ya fasa zuwa taron G20 saboda matsalar tsaro a NajeriyaYayin jawabi da ya gabatar a zauren majalisar a ranar Laraba, gwamnan ya ce an tsara kasafin ne don samar da sauye-sauye, kammala manyan ayyuka, inganta ilimi da harkar kiwon lafiya.
Ya bayyana cewa za a kashe Naira biliyan 934.6 (kashi 68) a manyan ayyuka kamar hanyoyi, gine-gine da sauran muhimman ayyuka.
Sauran Naira biliyan 433.4 (kashi 32), za su tafi ne a ayyukan yau da kullum.
Gwamna Abba ya ce ya aiwatar da kashi 80 na alƙawuran da ya yi a lokacin yaƙin neman zaɓe.
Ya ce kasafin 2026 zai mayar da hankali ne wajen kammala ayyuka a birane, faɗaɗa gidaje da kuma tallafa wa ƙananan masana’antu.
Ya fara jawabinsa da jajanta wa iyalan hamshaƙin attajiri Alhaji Aminu Alhassan Dantata, Galadiman Kano Alhaji Abbas Sanusi, da tsohon ɗan siyasa Alhaji Ahmadu Haruna Zago, waɗanda suka rasu a wannan shekara.
Hakazalika, ya yi jimamin rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da ’yan wasan Kano 22 da suka rasu a hatsarin mota a watan Mayu.
Abba, ya ce an aiwatar da kashi 75 na kasafin 2025 daga Janairu zuwa Oktoban wannan shekara, wanda a cewarsa an samu ci gaba mai kyau.
Ɓangaren ilimi ya samu Naira biliyan 280.6 (kashi 31) a 2025.
Ayyukan da aka yi sun haɗa da gyaran azuzuwa, shirye-shiryen ilimi kyauta, biyan kuɗin NECO, bayar da tallafin karatu, kafa Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Gaya, ɗaukar malaman darasin lissafi guda 400, masu gadi 1,600 da gyaran manyan makarantun sakandare.
Ya ce wannan ya taimaka wa Kano wajen zama ta farko a sakamakon NECO na 2025 a Najeriya.
A ɓangaren lafiya kuwa, gwamnatinsa ta kashe Naira biliyan 149.7 biliyan wajen gyara asibitoci a ƙananan hukumomi, inganta inshorar lafiya.
Sauran sun haɗa da ƙaddamar da shirin Abba-Care, gyaran cibiyoyi, da samar da kayan aikin lafiya da hanyoyin samar da wuta a manyan asibitoci.
Gwamnatinsa ta sayi buhun taki 199,000, ta raba wa al’umma shinkafa, ta amince da gina ƙananan madatsun ruwa 11, sannan ta ɗauki sababbin ma’aikatan aikin gona.
Ayyukan da aka yi sun haɗa da faɗaɗa tituna, siyan na’urar lantarki, saka fitilu a kan tituna, gyara masallatai, da samar da gidaje a sassa daban-daban na jihar.
Gwamnatin ta farfaɗo da cibiyoyin ɗinka kaya a ƙananan hukumomi 44, ta gyara manyan kasuwanni, ta tallafa wa ƙananan ’yan kasuwa, sannan ta shirya bukukuwan al’adu kamar KANFEST.
Haka kuma ta aiwatar da dokar canjin yanayi, ta share magudanan ruwa, ta sayi kayan sarrafa shara, ta kuma shuka bishiyoyi sama da miliyan 5.5.
Gwamna Abba, ya ce Hukumar Kula da Tsaro ta Jihar Kano, ta horar da jami’ai 2,000, ta kuma samar da kayan sintiri 6,000.
Matasa sama da 5,384 sun amfana da shirin tallafin Naira miliyan 800; dubban mata sun samu dabbobi; ƙananan ’yan kasuwa sun samu tallafin Naira 50,000 kowannensu.
A kasafin 2026, an raba jadawalin yadda kowane ɓangare zai samu:
Ilimi: Naira biliyan 405.3 (kashi 30) Lafiya: Naira biliyan 212.2 (kashi 16) Gine-gine: Naira biliyan 346.2 biliyan (kashi 25)Sauran sassa kamar noma, tsaro, kasuwanci, ruwa, muhalli da ci gaban matasa suma sun samu kuɗi mai yawa.
Gwamnan ya roƙi majalisar da ta hanzarta amincewa da kasafin, inda ya ce kasafin zai taimaka wajen samar wa al’ummar Kano ci gaba mai tarin yawa.
Ya gode wa ma’aikata, hukumomi, da al’ummar Kano kan goyon bayan da suke bai wa gwamnatinsa.
Kakakin Majalisar Dokokin jihar, Ismail Jibril Falgore, ya tabbatar da cewa majalisar za ta hanzarta amincewa da kasafin da zarar ta kammala nazarinsa.