Hukumar Alhazan Jihar Jigawa Ta Ware Kujeru 54 Ga Malamai Da Jami’an Kananan Hukumomi
Published: 18th, March 2025 GMT
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta bayyana cewa Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujeru 54 na Hajj ga malamai da jami’an da za su jagoranci Alhazai don aikin Hajjin 2025.
Babban Daraktan hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga wakilin Radio Nigeria a Dutse, babban birnin jihar.
A cewarsa, Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujerun ne domin bai wa jami’ai da malamai damar jagorantar Alhzan jihar a Najeriya da Saudiyya.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, wannan tsari da hukumar ta kirkiro shi ne irinsa na farko a tarihin Jihar Jigawa.
Ya bayyana cewa, an zabi jami’an da malamai maza da mata daga daga kananan hukumomi 27 na jihar bisa cancanta.
Ya jaddada cewa, an zaɓi mutum biyu daga kowace karamar hukuma ta jihar.
Babban Daraktan ya bayyana cewa, malamai da jami’an sun samu umarni don koyar da maniyyata game da wajiban Hajj, ka’idoji da kuma manyan ginshiƙan aikin Hajj domin su san yadda za su gudanar da ibadar Hajj yadda ya kamata.
Ya bayyana cewa, bayar da cikakken horo da ilimantar da maniyyata zai taimaka musu wajen gudanar da Hajj bisa koyarwar addinin Musulunci tare da wakiltar Najeriya da kyau.
Ya ƙara da cewa, za a ci gaba da gudanar da bita ga maniyyatan Hajj na 2025 a dukkan cibiyoyin da aka kebe bayan Ramadan.
Ahmed Labbo ya ce, hukumar za ta fara raba kayayyakin tafiya ga maniyyatan Hajj na 2025 nan ba da daɗewa ba.
A cewarsa, rarraba kayayyakin tafiya wadanda suka haɗa da yunifom da jakunkuna zai fara nan gaba a hedkwatar hukumar da wasu cibiyoyi da aka ware a faɗin kananan hukumomi 27 na jihar.
Ya bayyana cewa, jirgin farko na jigilar maniyyatan jihar zai tashi a watan Mayu 2025 kamar yadda Hukumar Hajj ta Kasa (NAHCON) ta tsara.
Labbo ya jaddada cewa, NAHCON ta ba Max Air damar jigilar maniyyatan jihar zuwa Saudiyya ta filin jirgin sama na Nuhu Muhammadu Sunusi International Airport.
Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan ya gode wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da haɗin kai da yake bai wa hukumar a kowane lokaci.
USMAN MUHAMMAD ZARIA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Ya bayyana cewa ya bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Harin Amurka ya bayyana karara kan Venezuela
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa: Barazanar da ake yi wa Venezuela ba ta dace da al’ummar duniya ba, yana mai jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta kasance kuma za ta ci gaba da kasancewa cikin hadin kai da gwamnati da al’ummar Caracas.
Da yake jawabi a bikin rantsar da ofishin wakilin Ma’aikatar Harkokin Waje a Lardin Hamadan, Araqchi ya bayyana cewa: Wannan ofishin zai taimaka wajen karfafa alakar tattalin arziki, kimiyya, da al’adu ta lardin, da kuma sauƙaƙe hulɗar jakadanci da gudanarwa ga ‘yan ƙasar.
Ya lura cewa: Baba’i Ragheb, wani jami’in ma’aikatar da ya ƙware, zai jagoranci sabon ofishin, kuma ya gode wa gwamnan Hamadan saboda haɗin gwiwarsa wajen samar da wurin zama na wucin gadi a cikin ginin gwamnatin. Ya ƙara da cewa a halin yanzu ana shirya wani gini daban, wanda nan ba da jimawa ba za a mayar da ofishin can.
Da yake amsa tambaya game da kalaman da jami’an Amurka suka yi kwanan nan game da Venezuela, Araqchi ya ce tsarin girman kai da kuma halayen Amurka sun bayyana a ko’ina cikin duniya. Ya bayyana cewa Amurka tana hulɗa ne kawai da ƙasashen da ke biyan muradunta kuma tana ƙiyayya da kowace ƙasa da ke ƙoƙarin samun ‘yancin kai, “kamar yadda ya kasance a Jamhuriyar Musulunci tsawon shekaru da dama.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Qalibaf: Iran Da Pakistan Zasu Aiwatar Dukkan Yarjejeniyar Da Suka Cimma A Tsakaninsu November 6, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Ce: Amurka Ta Bukaci Duba Kudurin Neman Kafa Rundunar Kasa Da Kasa A Gaza November 6, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Mutum Guda Tare Da Jikkata Wasu Uku A Kudancin Lebanon November 6, 2025 Sayyid Muqtada al-Sadr Ya Fadakar Da Magoya Bayansa Kwanaki Kafin Zabe A Iraki November 6, 2025 Araghchi : Yakin kwanaki 12 ya bamu babban darasi November 6, 2025 Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya November 6, 2025 Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Gwamnonin IAEA November 6, 2025 Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho November 6, 2025 Najeriya Ta Sake Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar November 6, 2025 Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya November 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci