Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta bayyana cewa Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujeru 54 na Hajj ga malamai da jami’an da za su jagoranci Alhazai don aikin Hajjin 2025.

Babban Daraktan hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga wakilin Radio Nigeria a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujerun ne domin bai wa jami’ai  da malamai damar jagorantar Alhzan jihar a Najeriya da Saudiyya.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, wannan tsari da hukumar ta kirkiro shi ne irinsa na farko a tarihin Jihar Jigawa.

 

Ya bayyana cewa, an zabi jami’an da malamai maza da mata daga  daga kananan hukumomi 27 na jihar bisa cancanta.

Ya jaddada cewa, an zaɓi mutum biyu daga kowace karamar hukuma ta jihar.

Babban Daraktan ya bayyana cewa,  malamai da jami’an sun samu umarni don koyar da maniyyata game da wajiban Hajj, ka’idoji da kuma manyan ginshiƙan aikin Hajj domin su san yadda za su gudanar da ibadar Hajj yadda ya kamata.

 

Ya bayyana cewa, bayar da cikakken horo da ilimantar da maniyyata zai taimaka musu wajen gudanar da Hajj bisa koyarwar addinin Musulunci tare da wakiltar Najeriya da kyau.

Ya ƙara da cewa, za a ci gaba da gudanar da bita ga maniyyatan Hajj na 2025 a dukkan cibiyoyin da aka kebe bayan Ramadan.

Ahmed Labbo ya ce, hukumar za ta fara raba kayayyakin tafiya ga maniyyatan Hajj na 2025 nan ba da daɗewa ba.

A cewarsa, rarraba kayayyakin tafiya wadanda suka  haɗa da yunifom da jakunkuna zai fara nan gaba a hedkwatar hukumar da wasu cibiyoyi da aka ware a faɗin kananan hukumomi 27 na jihar.

Ya bayyana cewa, jirgin farko na jigilar maniyyatan jihar zai tashi a  watan Mayu 2025 kamar yadda Hukumar Hajj ta Kasa (NAHCON) ta tsara.

Labbo ya jaddada cewa, NAHCON ta ba Max Air damar jigilar maniyyatan jihar zuwa Saudiyya ta filin jirgin sama na Nuhu Muhammadu Sunusi International Airport.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan ya gode wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da haɗin kai da yake bai wa hukumar a kowane lokaci.

 

USMAN MUHAMMAD ZARIA 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Ya bayyana cewa ya bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza

The Gaza Humanitarian Ffoundatin (GHF) a Gaza ta bada sanarwan kawo karshen ayyukanta a Gaza makonni 6 bayan an fara abinda suke kira tsagaita wuta a Gaza.

Shafin yana gizo na labarai ‘ArabNews’ na kasar Saudiya ya nakalto shugaban hukumar John Acree yana fadar haka ya kuma kara da cewa hukumar ta cimma manufar kafata na rarraba abinci tsakanin Falasdinawa a Gaza wadanda suke mutuwa saboda yunwa bayanda HKI ta hana shigowar abinci Gaza na tsawon kwanaki kimani 90 ko watanni 3.

Gwamnatin kasar Amurka ta da HKI ne suka kafa hukumar bada agajin bayan sun kori dukkan kungiyoyin bada agaji a yankin. Sannan sun yi amfani da hukumar don kissin Falasdinawa wadanda suke takawa da kafa zuwa cibiyoyin bada abinci da suka kafa a wuraren da sai sun wuta ta gaban sojojin HKI wadanda suke bude masu wuta. Amma Falasdinawan basu da zabi ko yunwa ta kashe su a cikin gaza ko kuma su je su karbi abincin da mai yuwa ba zasu dawo ba har abada.

Amurka da HKI sun kashe daruruwan Falasdinawa a cikin wannan lokacin.  Acree yace sun raba  kunshi miliyon uku dauke da abinci miliyon 187 ga falasdinawa a lokacin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Tsirin Trump Na Zaman Lafiya November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare   November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Wakilin MDD Ya Bukaci Goyon Bayan Iran Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yamen November 24, 2025 Yara 50 Da Aka Sace A Najeriya Sun Tsere Daga Hannun Barayin Daji November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja
  • Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kwara Ta Sanar da Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajjin 2026
  • Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi
  • Iran ta sake tir da sabon kudurin da Hukumar (IAEA)