Hukumar Alhazan Jihar Jigawa Ta Ware Kujeru 54 Ga Malamai Da Jami’an Kananan Hukumomi
Published: 18th, March 2025 GMT
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta bayyana cewa Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujeru 54 na Hajj ga malamai da jami’an da za su jagoranci Alhazai don aikin Hajjin 2025.
Babban Daraktan hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga wakilin Radio Nigeria a Dutse, babban birnin jihar.
A cewarsa, Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujerun ne domin bai wa jami’ai da malamai damar jagorantar Alhzan jihar a Najeriya da Saudiyya.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, wannan tsari da hukumar ta kirkiro shi ne irinsa na farko a tarihin Jihar Jigawa.
Ya bayyana cewa, an zabi jami’an da malamai maza da mata daga daga kananan hukumomi 27 na jihar bisa cancanta.
Ya jaddada cewa, an zaɓi mutum biyu daga kowace karamar hukuma ta jihar.
Babban Daraktan ya bayyana cewa, malamai da jami’an sun samu umarni don koyar da maniyyata game da wajiban Hajj, ka’idoji da kuma manyan ginshiƙan aikin Hajj domin su san yadda za su gudanar da ibadar Hajj yadda ya kamata.
Ya bayyana cewa, bayar da cikakken horo da ilimantar da maniyyata zai taimaka musu wajen gudanar da Hajj bisa koyarwar addinin Musulunci tare da wakiltar Najeriya da kyau.
Ya ƙara da cewa, za a ci gaba da gudanar da bita ga maniyyatan Hajj na 2025 a dukkan cibiyoyin da aka kebe bayan Ramadan.
Ahmed Labbo ya ce, hukumar za ta fara raba kayayyakin tafiya ga maniyyatan Hajj na 2025 nan ba da daɗewa ba.
A cewarsa, rarraba kayayyakin tafiya wadanda suka haɗa da yunifom da jakunkuna zai fara nan gaba a hedkwatar hukumar da wasu cibiyoyi da aka ware a faɗin kananan hukumomi 27 na jihar.
Ya bayyana cewa, jirgin farko na jigilar maniyyatan jihar zai tashi a watan Mayu 2025 kamar yadda Hukumar Hajj ta Kasa (NAHCON) ta tsara.
Labbo ya jaddada cewa, NAHCON ta ba Max Air damar jigilar maniyyatan jihar zuwa Saudiyya ta filin jirgin sama na Nuhu Muhammadu Sunusi International Airport.
Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan ya gode wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da haɗin kai da yake bai wa hukumar a kowane lokaci.
USMAN MUHAMMAD ZARIA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Ya bayyana cewa ya bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Wannan shi ne daya daga cikin martanin NASENI da abokan huldarta don samar da CNG, wannan kuma na daga shirin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na daƙile tasirin cire tallafin man fetur ta hanyar samar da iskar gas mai rahusa.
Manufar ita ce a rage dogaro da na’urorin lantarki da ake shigowa da su daga waje, da inganta dogaro da kai a ɓangaren fasaha, da samar da ayyukan yi. NASENI tana ba da ababen more rayuwa da tallafin manufofin, yayin da ɓangaren da ke kula da masana’antu, yana mai da hankali kan haɗin gwiwa, ƙirƙira da kasuwanci don kafa Nijeriya a matsayin cibiyar fasahar Afirka.
Wannan dabarar da NASENI ta yi ya tabbatar da cewa ba a bar kasar a baya ba a cikin juyin juya halin masana’antu da ke faruwa a duniya a halijn yanzu.
NASENI na zuba jari mai yawa wajen bincike a ɓangaren ayyukan da ake yi na yanayi mai dorewa a Nijeriya domin bunkasa tattalin arzikin ƙasa kamar yadda yake a tsare staren tattalin arziƙin shugaba Bola Ahamed Tinubu.
Hukumar NASENI ta haɗa kai da gwamnatin Jamhuriyar Czech domin raba jimillar dala miliyan 21.7 ga zababbun mutane 11 da za su ci gajiyar ayyukan Delta-2 don fara aiwatar musayar fasahohin zamani zuwa Nijeriya. Shirin Delta-2 shi ne samfurin haɗin gwiwar Hukumar Fasaha ta Jamhuriyar Czech (TA CR) ta hanyar da TA CR ke tallafa wa aiwatar da bincike da haɓaka masana’antu da cibiyoyi masu ƙima. An ƙaddamar da shi ne a cikin shekarar 2021, shirin Delta-2 yana ba da kuɗi kuma yana ba da damar bincike da haɓaka ayyukan ƙirƙire- ƙieƙire a fannoni uku da aka mayar da hankali: aikin gona, ma’adinai, da masana’antu gaba ɗaya.
Samar da famfon ban ruwa mai amfani da hasken rana na NASENI ya kawo sauyi ga harkar noma ta hanyar inganta noman rani. Yanzu haka manoman Nijeriya suna amfana ta hanyoyi daban-daban daga wannan fanfo mai sauƙin gaske wanda ke samar da ingantaccen ruwa na amfanin gona. Manoma za su iya amfani da famfon ban ruwa mai amfani da hasken rana don samar da amfanin gona akai-akai, wanda hakan zai bunƙasa yawan amfanin gona da kuma girbi da yawa a kowace shekara.
Yana sa manoma su rage dogaro da yanayin ruwan sama maras tabbas, don haka yana rage haɗarin gazawar amfanin gona. Yana kawar da dogaro da man dizal ko man fetur don ban ruwa tare da rage hayakin iskar gas da gurɓataccen muhalli. Hakanan za a iya amfani da shi a wuraren da basa tare da babbar hanyar wutaingantaccen hanyar grid ba. Ta hanyar amfani da famfunan ban ruwa mai amfani da hasken rana na NASENI, manoma suna ƙara haɓaka aikin noma sosai, da rage tsadar aiki, da samun ƙarin kuɗin shiga da inganta rayuwa idan aka kwatanta da famfunan ban ruwa masu amfani da man fetur.
Domin wannan ci gaba mai ɗorewa na ci gaban masana’antun Nijeriya da kuma tsara makomar al’ummar ta hanyar dogaro da kai, NASENI ce Gwarzon Kamfanin LEADERSHIP na shekarar 2025.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA