Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta bayyana cewa Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujeru 54 na Hajj ga malamai da jami’an da za su jagoranci Alhazai don aikin Hajjin 2025.

Babban Daraktan hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga wakilin Radio Nigeria a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, Gwamna Umar Namadi ya amince da rabon kujerun ne domin bai wa jami’ai  da malamai damar jagorantar Alhzan jihar a Najeriya da Saudiyya.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya ce, wannan tsari da hukumar ta kirkiro shi ne irinsa na farko a tarihin Jihar Jigawa.

 

Ya bayyana cewa, an zabi jami’an da malamai maza da mata daga  daga kananan hukumomi 27 na jihar bisa cancanta.

Ya jaddada cewa, an zaɓi mutum biyu daga kowace karamar hukuma ta jihar.

Babban Daraktan ya bayyana cewa,  malamai da jami’an sun samu umarni don koyar da maniyyata game da wajiban Hajj, ka’idoji da kuma manyan ginshiƙan aikin Hajj domin su san yadda za su gudanar da ibadar Hajj yadda ya kamata.

 

Ya bayyana cewa, bayar da cikakken horo da ilimantar da maniyyata zai taimaka musu wajen gudanar da Hajj bisa koyarwar addinin Musulunci tare da wakiltar Najeriya da kyau.

Ya ƙara da cewa, za a ci gaba da gudanar da bita ga maniyyatan Hajj na 2025 a dukkan cibiyoyin da aka kebe bayan Ramadan.

Ahmed Labbo ya ce, hukumar za ta fara raba kayayyakin tafiya ga maniyyatan Hajj na 2025 nan ba da daɗewa ba.

A cewarsa, rarraba kayayyakin tafiya wadanda suka  haɗa da yunifom da jakunkuna zai fara nan gaba a hedkwatar hukumar da wasu cibiyoyi da aka ware a faɗin kananan hukumomi 27 na jihar.

Ya bayyana cewa, jirgin farko na jigilar maniyyatan jihar zai tashi a  watan Mayu 2025 kamar yadda Hukumar Hajj ta Kasa (NAHCON) ta tsara.

Labbo ya jaddada cewa, NAHCON ta ba Max Air damar jigilar maniyyatan jihar zuwa Saudiyya ta filin jirgin sama na Nuhu Muhammadu Sunusi International Airport.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan ya gode wa Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da haɗin kai da yake bai wa hukumar a kowane lokaci.

 

USMAN MUHAMMAD ZARIA 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Ya bayyana cewa ya bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi

Gwamnatin Jihar Bauchi, ta ƙaryata zargin cewa Gwamna Bala Mohammed na shirin ficewa daga PDP zuwa jami’yyar PRP.

Jita-jitar ta samo asali ne bayan Sakataren jam’iyyar PRP na Bauchi, Hon. Wada Abdullahi, ya ce ba za su karɓi gwamnan zuwa jami’yyarsu ba.

Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky

Ya ce gwamnan bai cika ƙa’idojin da PRP ke buƙata ba a shugabancinsa a Bauchi.

Amma mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin yaɗa labarai, Mukhtar Gidado, ya ce gwamnan bai taɓa tunanin barin PDP ba.

Ya ce babu wata tattaunawa ko mataki da aka ɗauka na komawa PRP.

Gidado, ya ce gwamnan na aiki ne wajen ƙarfafa PDP kuma ya taɓa doke PRP a zaɓuka da suka gabata.

Ya ƙara da cewa Jihar Bauchi ta samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnan, musamman a ɓangaren tallafa wa jama’a, ababen more rayuwa, ci gaban ƙauyuka, da yawon buɗe ido.

Gwamnatin ta soki PRP kan yaɗa jita-jita marasa tushe.

Ya ce gwamnan na da ’yancin zaɓar makomarsa a harkokin siyasa, amma duk wata shawara da zai ɗauka ba za ta kasance bisa ƙarya ko jita-jita ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Fara Gyaran Tashar Talabijin Ta Jigawa Don Kara Mata Nisan Zango
  • Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa ta Kiyasta Naira Biliyan 3 Don Ayyukan Hajjin 2026
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha