HKI Ta Nuna Damuwarta Da Jibge Sojojin Da Gwamnatin Masar Ta Yi A Yankin Sina
Published: 18th, March 2025 GMT
Gwamnatin HKI ta bayyana damuwarta da jibge sojojin da gwamnatin kasar masar take yi a yankin Sinaa kusa da kan iyakar kasar da HKI.
Tun bayan da gwamnatin HKI ta gama lalata makaman gwamnatin kasar Siriya bayan ta taimaka ta kawo dan Daesh kan kujerar shugabancin kasar ta Siriya, kuma ta bayyana cewa yankunan da ta mamaye a kasar Siriya sun zama HKI ne har abada.
Banda haka mun ga yadda sabon shugaban kasar ta Siriya Julani ya yi shiri da bakinsa a kan mamayar da HKI takewa kasar Siriya da kuma yadda ta kai hare-hare fiye da dubu guda kan kasar tana lalata makamanta, ko wa ya fahinci cewa, siriya ta gama yawo,. Kuma ba zata taba daga ko tsinke a gaban HKI ba.
Tashar talabijin ta Presstv ba ce, a halin yanzu hankalin yahudawa ya koma kan kasar Masar, wacce take ganin bangare na HKI kuma kasar tana iya zama matsala gareta, duk tare da nasarorin da ta samu ya zuwa yanzu na mamayar kasashen larabawa.
Tsohon babban haffsan sojojin HKI Herzi Halevi ya fito fili ya na cewa suna cikin damuwa dangane da kasar Masar. Don ta sami ci gaba sosai a bangaren mallakan makamai na zamani.
Ya kuma kara da cewa, a shekara ta 2011 da aka yi juyin juya halin na yanuwa musulmi, wato Muhammad Mursi sun ji tsaro, amma sun dan numfasa bayan an kauda Mursi. Sai dai a halin yanza akwai barazana na kara karfi a bangaren kasar ta Masar, musamman bayan yakin 7 ga watan Octoba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Masar
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Jiang Bin, ya ce a baya bayan nan babban jirgin ruwan dakon jiragen sama na kasar Sin mai suna Fujian, ya doshi yankin tekun kudancin kasar, inda ya ratsa ta zirin Taiwan, a kan hanyarsa ta gudanar da gwaje-gwaje da samar da horo.
Jami’in wanda ya bayyana hakan a Talatar nan, ya ce hakan bangare ne na ayyukan da aka saba gudanarwa lokaci-lokaci a wani bangare na kirar jirgin.
Jiang Bin, ya yi tsokacin ne yayin da yake amsa wata tambaya mai nasaba da hakan da aka yi masa, yana mai cewa, bulaguron jirgin ya dace da dokokin kasa da kasa da ayyuka masu nasaba, kuma ba shi da wata nasaba da tunkarar wani sashe. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp