Aljeriya Ta Kori Jami’an Diflomasiyya Faransa 12
Published: 15th, April 2025 GMT
Gwamnatin kasar Ajeriya ta bayyana jami’an diflomasiyyar Faransa da suke kasar su 12 a matsayin ‘wadanda ba a bukatar ganinsu” a cikin kasar, tare da yin kira a gare su da su fice a cikin sa’oi 48.
Bugu da kari kasar ta Aljeriya ta yi suka da kakkausar murya akan ministan harkokin wajen Faransa Bruno Rotayo,tare da cewa za ta mayar masa da martanin da ya dace.
Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Aljeriya ta bayyana cewa; A matsayinta na kasa mai cikakken shugabanci, tana daukar ma’aikatan ofishin jakadanci Faransa 12 a matsayin wadanda ba a maraba da su, sannan kuma ana bukatar da su fice daga kasar a cikin sa’oi 48.”
Aljeriya din ta dauki wannan matakin ne a matsayin mayar da martani ga kama wani jami’in diflomasiyyarta da aka yi a kasar Faransa a ranar 8 ga watan Aprilu da ake ciki.
Aljeriyan ta bayyana abinda ya faru da cewa, keta hurumin kasarta ne da kuma take dokokin aikin diflomasiyya.”
Haka nan kuma ta yi ishar da cewa, ma’aikacin diflomasiyyar da aka kama yana da kariya ta aiki wacce ta hana a yi masa abinda ya faru,amma kuma gwamnatin Faransa ta yi mu’amala a shi ta hanya mafi muni da halayya irin ta barayi.’
Alaka a tsakanin Faransa da Aljeriya tana kwan-gaba da baya, musamman a cikin watannin bayan nan. Watanni 8 da su ka gabata an sami rashin jituwa a tsakaninsu saboda korar wasu ‘yan asalin Aljeriya mazauna Faransa bisa zargin cewa sun shiga kasar ba bisa ka’ida ba. Aljeriya ta yi wa jakadanta kiranye, tare da rufe kafar diflomasiyya a tsakaninsu na tsawon watanni 8.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Aljeriya ta
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
Dakarun kare juyin musulunci na Iran sun fitar da bayani a lokacin tunawa da sace jami;an diplomasiyyar Iran 4 a birnin Beirut, wanda ya kunshi cewa: Ya zama wajibi ‘yan sahayoniya su kwana da sanin cewa; Duk laifukan da su ka aikata a baya za a yi musu sakamako a kansa,kuma duk wani sabon wuce gona da iri, zai gaggauta zuwa karshensu ne.”
Sanarwar ta kuma ce: Muna tunawa ne da zagayowar cikar shekaru 42 daga wancan aikin ta’addanci, da a yanzu kwanaki kadan ne su ka wuce na kawo karshen yakin da HKI da Amurka su ka kallafa mana na tsawon kwanaki 12. Yaki ne wanda martani mai karfi da jamhuriyar musulunci ta Iran ta mayar yake kara fito da raunin da wannan kirkirarriyar kasa take da shi.
Har ila yau bayanin na dakarun kare juyin musulunci na Iran ya bayyana yadda jamhuriyar musulunci ta Iran ta yi ta kokari a fagen diplomasiyya akan batun jami’an diplomasiyyar da Isra’ila ce ta sace su ta hanyar ‘yan korenta,kuma hatta babban magatakardar MDD a 2008 ya bayyana cewa a shirye yake ya bayar da hadin kai domin ganin an warware batun,amma kuma abin takaici har zuwa yanzu wadanda su ka aikata laifin ba su fuskanci sakamakon da ya dace da su ba.
A dalilin haka dakarun kare juyin musuluncin suke kara tunatar da MDD da kuma kungiyar agaji da “Red Cross” da su yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyansu akan wannan batun. jami’an diplomasiyyar da HKI ta yi garkuwa da su sun hada janar Alhaj Ahmad Mutawassiliyan, sai Sayyid Muhsin Musawi, Taki Rastigar Mukaddam, da kuma Kazim Akawan.