Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-07-11@09:00:01 GMT

Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa

Published: 15th, April 2025 GMT

Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa

Tsangayar Ilimi na Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ya shirya wani taron bikin cika shekaru 50 da kafuwa tare da gudanar da taron kasa karo na uku.

Taron wanda aka yi wa take da “Ilimi Mai Sauya Rayuwa Don Gaba: Fuskantar Sabbin Kalubale da Buɗe Damar Samun Ci gaba” ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki daga sashen ilimi.

Da take jawabi a wajen taron, Minista a ma’aikatar Ilimi Farfesa Suwaiba Ahmed Sa’id ta bayyana cewa, a ƙoƙarin da gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ke yi na ƙarfafa tsarin ilimi, ya amince da kashe Naira biliyan 120 don bunƙasa shirin fasaha da koyon sana’o’i (TVET) a Najeriya.

Ministar ta kuma bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta amince da fitar da Naira biliyan 40 domin kammala aikin ɗakin karatu na ƙasa da aka yi watsi da shi, domin tallafawa bincike da cigaban karatu.

Farfesa Suwaiba ta ƙara da cewa, ma’aikatar ilimi ta tarayya ƙarƙashin jagorancin Minista Alausa ta ƙaddamar da Shirin Sabunta Hanyar Ilimi ta Najeriya (NESRI).

“Ina da burin mayar da Najeriya daga tattalin arzikin da ke dogara da albarkatu zuwa tattalin arzikin da ke dogara da ilimi, tare da rage yawan yara da ba sa zuwa makaranta, rage ƙarancin koyo, da samun  ƙara ƙwarewa.”

Yayin da yake buɗe taron, Shugaban Jami’ar Bayero Kano, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya bayyana nasarorin da sashen ya samu, inda ya ce ya samar da manyan mutane kamar ministocin ilimi biyu, shugabannin jami’o’i tara, da matan gwamnan jihar Kano guda uku, da sauran fitattun ’yan Najeriya da suka yi fice a fannoni daban-daban.

Yayin da yake yabawa taken taron da dacewarsa, Farfesa Sagir ya tabbatar da cewa jami’ar tana nan daram wajen tallafawa duk wani shiri da zai ɗaga matsayin ilimi zuwa na ƙasa da ƙasa.

A jawabinsa na maraba, Shugaban tsangayar Ilimi na Jami’ar Bayero Kano (BUK), Dakta Abubakar Ibrahim Hassan, ya jaddada yadda tsangayar ke  kokari wajen shirya harkokin ilimi da na kimiyya.

“Daga cikin nasarorin da Jami’ar BUK ta samu a kwanan nan akwai samun tallafin TETFUND guda biyu da kowanne ya haura naira biliyan 30, tare da lashe wani shirin koyar da harsuna biyu wanda Bankin Raya Musulunci da Hukumar Ilimin Firamare ta Kasa (UBEC) suka dauki nauyi.”

Taron ya yi armashi inda aka bayar da lambar yabo ga fitattun ‘yan Najeriya da suka hada da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da matarsa Farfesa Hafsat, da Minista a ma’aikatar Ilimi ta Jiha Farfesa Suwaiba, tsohuwar Ministar Ilimi Farfesa Rukayya, da Farfesa Isah Yahaya Bunkure da wasu da dama.

Daga Khadija Aliyu 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

 Masu Kare Hakkin Dan’adam Suna Allawadai Da Takunkumin Amurka  Akann Jami’ar MDD A Falasdinu

Kungiyoyin kare hakkin dan’adam suna yin tir da takunkumin da Amurka ta kakaba wa Francesca Albanese wacce it ace jami’ar MDD mai kula da hakkokin bil’adam a Falasdinu.

Shugaban cibiyar siyasar kasa da kasa da ta shafi hukumomi Dylan Williams ya bayyana takunkumin da cewa; Yana nuni da da halayyar gwamnatin ‘yan daba’.

Ita kuwa shugabar kungiyar kare hakkin bil’adama ta kasa da kasa “Amnesty International” Agnès Callamard kira ta yi ga gwamnatocin duniya da dukkanin masu bakin fada da su ka yi Imani da aiki da dokokin kasa da kasa da su yi duk abinda za su iya, domin ganin an hana takunkumin yin tasiri akan ayyukan Francesca Albanese, da kuma bayar da kariya ga dukkanin aikin hukumar ta kare hakkin dan’adam da kare ‘yancinsu.”

A jiya Laraba ne dai Amurka ta kakaba takunkumi akan Francesca Albanese saboda ta soki yakin da  Isra’ila take yi a Gaza.

Ministan harkokin wajen Amurka Marco Rubio ne ya bayyana cewa: “A yau ina mai sanar da kakaba takunkumi na musamman akan jami’ar kula da hakkin dan’adam ta MDD Francesca Albanese, saboda ayyukan da take yi da su ka saba doka na Sanya kotun manyan laifuka ta duniya daukar matakan da suke cin karo da doka aakn kamfanoni da jami’ai na Amurka da Isra’ila.”

Francesca Albanese ta mayar da martani a sahfinta na X cewa: A cikin karsashi da gamsuwa, zan kasance a tare da adalci, kamar kowane lokaci.”

A wani rahoto da ta fitar jami’ar kare hakkin bil’adaman ta MDD ta zargi manyan  kamfanonin  fasahar zamani  fiye da 60 da masu kera makamai da suke taimakawa ‘yan share wauri zauna a Isra’ila da kuma yakin da suke yi a Gaza. Haka nan kuma ta yi kira ga wadannan kamfanonin da su dakatar da taimakawa Isra’ila da suke yi, sannan kuma ta bukaci ganin an hukunta manajojin wadannan kamfunan saboda keta dokokin kasa da kasa da suke yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki
  •  Masu Kare Hakkin Dan’adam Suna Allawadai Da Takunkumin Amurka  Akann Jami’ar MDD A Falasdinu
  • Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
  • An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos
  • Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawa
  • Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 30 a Katsina
  • Sojojin Yemen Sun Nutsar Da Jirgin Ruwan “Eternity” Dake Hanyar Zuwa HKI
  • Biza: UAE ta ƙaƙaba wa ’yan Najeriya sabbin takunkumai
  • Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki
  • Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC