’Yan bindiga sun kai hari a kan taron masu ibada inda suka yi awon gaba da mutane da dama da ba a tantance ainihin yawansu ba.
Mutane suna tsaka da gudanar da ibadar dare ne a kan wani tsauni a lokacin da ’yan bindigar suka kai musu farmakin suka yi garkuwa da su.
Lamarin ya auku ne a ranar Juma’a yankin Egbola, a kan hanyar Agabja a Ƙaramar Hukumar Lokoja.
Shaidu sun bayyana cewa ’yan bangan gwmanatin jihar sun yi nasarar ceto wata mata daga cikin masu ibadan, bayan sun samu rahoton aukuwar lamarin.
NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙuraWani ɗan banga daga cikin waɗanda suka kai ɗauki ya bayyana cewa matar ta tsere ne bayan da ’yan bindigar suka kawo harin, daga bisani ’yan bindigar suka tsince ta.
Wakilinmu ya yi ƙoƙarin yin magana da mai magana da yawun ’yan sanda a Jihar Kogi, ASP William Aya, amma jami’in bai amsa ko ɗaya daga cikin kiraye-kirayen wayan wakilin namu ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga awon gaba Garkuwa ibadar dare Jihar Kogi
এছাড়াও পড়ুন:
Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
Tafarkin samun ci gaba mai karfi da inganci, da karuwar kuzarin kirkire-kirkire da ci gaba da fadada bude kofa, su ne suka hadu suka samar da wani sabon matsayi ga tattalin arzikin kasar Sin a taswirar tattalin arzikin duniya. Ci gaba mai inganci da fadada bude kofa, ba muhimman jigon ne dake ingiza tattalin arzikin Sin kadai ba, har da nuna yanayin sauyawar abubuwan dake haifar da ci gaba a duniya. Wani nazari da kafar CGTN ta gudanar ta kafar intanet, ya nuna yadda masu bayar da amsa daga fadin duniya suka yi imanin cewa, tattalin arzikin Sin ya samu ci gaba ta kowace fuska ba tare da tangarda ba, lamarin da ya samar da tabbaci ga tattalin arzikin duniya.
Karfin tattalin arzikin Sin ya dagora ne da sabon karfin samar da hajoji da hidimomi da ke samun ci gaba cikin sauri, wadda ake ganin saurin ci gabanta ta hanyar kirkire-kirkire. Nazarin ya nuna cewa, kaso 93.6 na wadanda suka bayar da amsa, sun yi imanin cewa, kirkire-kirkire na taka muhimmiyar rawa wajen raya tattalin arziki mai inganci na Sin. Wasu kaso 96.6 kuma sun yi imanin cewa, kasar Sin na jagorantar manyan sauye-sauye a tsare-tsaren tafiyar da masana’antu da na tattalin arziki ta hanyar kirkire kirkiren kimiyya da fasaha.
A matsayinta na kasa ta biyu mafi yawan masu sayayya, kasar Sin ce ke da mutane masu matsakaicin kudin shiga mafi yawa a duniya, inda take da gagarumin karfin sayayya da na zuba jari. Nazarin ya nuna cewa, kaso 82.3 na masu bayar da amsu sun yi imanin cewa, kamfanonin kasashen waje za su iya amfani da fa’idojin da suke da shi wajen shiga kasuwar kasar Sin domin kara samun karfin takara a duniya. (FMM)
ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA