Aminiya:
2025-12-07@10:20:05 GMT

An yi garkuwa da masu ibada a Kogi

Published: 15th, April 2025 GMT

’Yan bindiga sun kai hari a kan taron masu ibada inda suka yi awon gaba da mutane da dama da ba a tantance ainihin yawansu ba.

Mutane suna tsaka da gudanar da ibadar dare ne a kan wani tsauni a lokacin da ’yan bindigar suka kai musu farmakin suka yi garkuwa da su.

Lamarin ya auku ne a ranar Juma’a yankin Egbola, a kan hanyar Agabja a Ƙaramar Hukumar Lokoja.

Shaidu sun bayyana cewa ’yan bangan gwmanatin jihar sun yi nasarar ceto wata mata daga cikin masu ibadan, bayan sun samu rahoton aukuwar lamarin.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura

Wani ɗan banga daga cikin waɗanda suka kai ɗauki ya bayyana cewa matar ta tsere ne bayan da ’yan bindigar suka kawo harin, daga bisani ’yan bindigar suka tsince ta.

Wakilinmu ya yi ƙoƙarin yin magana da mai magana da yawun ’yan sanda a Jihar Kogi, ASP William Aya, amma jami’in bai amsa ko ɗaya daga cikin kiraye-kirayen wayan wakilin namu ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga awon gaba Garkuwa ibadar dare Jihar Kogi

এছাড়াও পড়ুন:

Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas

Hukumar Kwastam, ta kama kilo 25.5 na hodar iblis a wani jirgin ruwa na ƙasar Brazil mai suna MV San Anthonio a tashar jirgin ruwa ta Legas.

An ɓoye hodar cikin ƙananan jakunkuna biyar.

’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —Gwamnati

Kwanturola Emmanuel Oshoba, ya ce an gudanar da aikin ne bayan samun bayanan sirri tare da haɗin gwiwar hukumar NDLEA.

Ya ƙara da cewa jirgin ya tsaya a ƙasashen da suka yi ƙaurin suna wajen harkar safarar miyagun ƙwayoyi kafin isowarsa Najeriya.

An tsare jirgin, sannan an miƙa hodar da aka kama ga NDLEA domin ci gaba da bincike.

Oshoba, ya ce wannan nasara tana nuna jajircewar hukumar Kwastam wajen kawar da haramtattun kasuwanci da kuma kare ƙasa, musamman lokacin bukukuwan ƙarshen shekara ke ƙaratowa.

Ya yi gargaɗin cewa hukumar ba za ta bari a yi amfani da ita wajen aikata laifuka ba, kuma duk kayayyakin da suka shigo da su sai an yi bincike a kansu.

A cewarsa, haɗin kai tsakanin Kwastam da NDLEA yana bayar da kyakkyawan sakamako, kuma zai ci gaba da karya tsarin masu safarar miyagun ƙwayoyi.

Jami’an NDLEA ƙarƙashin jagorancin CN Haliru Umar sun karɓi kayan da aka kama.

Kwastam ta kuma buƙaci masu mu’amala da tashar su kasance masu bin doka tare da kai rahoton duk wani abun zargi domin tabbatar da tsaron tashar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • ’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Nigeria: Har Yanzu Da Akwai Daliban Makaranta 250 Da Suke Hannun Masu Garkuwa Da Su
  • Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • An harbe manomi saboda rikici kan filin kiwo a Borno
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15