“Abin takaici ne cewa, a maimakon yin amfani da gagarumin goyon baya da yunƙurin da ƴan ƙasa ke ginawa, Onanuga ya zaɓi fitar da wata sanarwa mai takurawa. Fahimtar da ya yi wa dokar zabe yana da tsauri fiye da kima kuma ya kasa gane bambanci tsakanin yakin neman zabe ba bisa ka’ida ba da kuma furuci na siyasa na gaske na ‘yan kasa.

 

“Ƙungiyar gamayyar matasan Arewa ta yi watsi da wannan mataki. Goyon baya ga Shugaba Tinubu na halitta ne kuma a duk faɗin ƙasar, Ginin siyasa ba laifi ba ne.

 

“Don haka, muna kira da a gaggauta maye gurbin Bayo Onanuga, mai bayar da shawara kan harkokin siyasa da kuma mai bayar da shawara ga kafofin watsa labaru wanda da wanda ya fahimci halin da mutane ke ciki kuma zai iya amfani da dabarar ginin siyasa”. In ji Galadiman Takai.

 

In ba a manta ba, mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ya ce, akwai alluna dauke da hotunan shugaban kasa da na matarsa, Sanata Oluremi Tinubu, musamman a Abuja da kuma jihar Kano, da ke kama da fara gangamin yakin neman zabe.

 

A cewar Onanuga, shugaba Tinubu da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettim na matukar godiya ga dimbin magoya bayansu a fadin kasar nan saboda himima da ci gaba da goyon bayansu, amma shugabannin biyu ba sa goyon bayan duk wani gangamin yakin neman zabe da ya saba wa dokokin kasar nan.

 

Ya ce, dokar zaɓe da ke jagorantar gudanar da zaɓe da yaƙin neman zaɓe, ta haramta duk wani nau’i na yaƙin neman zaɓe na 2027 a wannan lokaci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin

Majalisar Dattawa a ranar Talata ta amince da bukatar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin domin tabbatar da dimokuradiyya a kasar.

Majalisar ta kuma ce tana goyon bayan matakin da shugaban ya ɗauka kwanaki kafin haka domin hana yunƙurin kifar da tsarin dimokuraɗiyya a makwabciyar kasar.

Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta

Bukatar dai na kunshe ne a cikin wata wasiƙa da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio, ya karanta a zauren majalisa yayin zamanta.

Tinubu ya umarci tura sojojin makon da ya gabata domin dakile yunƙurin karɓar mulki ba bisa ka’ida ba a Jamhuriyar Benin da kuma kaucewa rikicewar tsaro a yankin yammacin Afirka.

Sai dai Tinubu bai nemi amincewar majalisa ba kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Bayan karanta wasiƙar, majalisar ta koma zaman kwamiti domin tantance bukatar. A yayin zaman, ’yan majalisa sun tattauna kan tasirin tsaro, jin‑ƙai da diflomasiyya da ke tattare da wannan mataki.

Babbar damuwar a cewarsu ta haɗa da yiwuwar kwararar ’yan gudun hijira zuwa Najeriya, tsaron iyaka da kuma tasirin matakin ga zaman lafiya da tsaro a yankin.

Bayan doguwar muhawara, majalisar ta koma zama a zaurenta, inda ta kada kuri’ar amincewa da matakin shugaban ƙasa cikin rinjaye.

Shugaban Majalisar, Akpabio, ya gabatar da rahoton kwamitin domin tabbatarwa, inda ’yan majalisa suka amince ba tare da wata adawa ba kafin su amince da tura sojojin ta hanyar kada kuri’ar murya karo na biyu.

A jawabin sa, Akpabio ya yabawa Shugaba Tinubu bisa ɗaukar matakan da suka tabbatar da zaman lafiya a yankin da kuma bin ka’idojin kundin tsarin mulki ta hanyar neman amincewar majalisa, ko da bayan tura sojojin cikin gaggawa.

“Wannan mataki ne da ya zama dole. Shugaban Ƙasa ya yi aiki ne domin kare tsaron ƙasa da kuma kare dimokuraɗiyya a yammacin Afirka. Barazana ga kasa ɗaya barazana ce ga kowa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa za a isar da kudurin majalisar ga Shugaban Ƙasa nan take.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jigawa Ta Nemi Kotuna Su Daina Jan Kafa Wajen Aiwatar da Shari’a
  • Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda
  • Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Ya Isa Abidjan Wajen Rantsar da Shugaba Ouattara
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin