HausaTv:
2025-06-15@18:17:42 GMT

Pezeshkian: Babu Batun Tattaunawa Da Amurka A Karkashin Matsin Lamba

Published: 12th, March 2025 GMT

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi kakkausar suka ga matakin da gwamnatin Trump ya dauka kan Iran, yana mai bayyana cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba Ukraine ba ce, kuma ba za ta yi shawarwari da Amurka bisa barazana ko tilasci  ba.

“Dole ne mu kiyaye dangantaka da duniya. Ba ma son mu yi sabani ko jayayya da kowa, amma hakan ba yana nufin za mu durkusa cikin wulakanci a gaban kowa ba,” in ji Pezeshkian yayin wani taron kungiyar ‘yan kasuwan Iran a Tehran a ranar Talata.

“Muna iya mutuwa da daraja, amma ba za mu taɓa rayuwa cikin kunya da kaskanci ba.”

Pezeshkian ya yi watsi da abin da ya bayyana a matsayin wa’adi daga Donald Trump, yana mai nuni da wata wasika da aka ce shugaban Amurka ya aike zuwa Iran.

Wasikar ta bukaci Tehran da ta dakatar da shirye-shiryenta na nukiliya da makamai masu linzami da kuma daukar wasu matakai domin samun sassaucin takunkumi.

Ya soki Trump da rashin mutunta takwaransa na Ukraine, Volodymyr Zelensky, yayin da ya matsa masa lamba kan ya amince da wata yarjejeniya da Rasha.

Shugaban na Iran ya ce halin da Trump ya nuna a ganawarsa da  Zelensky a fadar White House abin kunya ne.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje

Lamarin ya ci gaba da raguwa har zuwa 2024, inda yawan kudaden da ake kashewa a yawon ketare ya fadi da kaso 14 a matakin shekara-shekara zuwa dala biliyan 2.66.

Hakan na nuni da cewa ‘yan Nijeriya sun rage kashe kudaden da suke kashewa kan safarar jiragen sama da dala biliyan 1.12 ko kuma kashi 30 cikin dari a cikin shekaru biyun.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa