Aminiya:
2025-12-04@18:22:22 GMT

Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mai juna biyu da wasu mutum 10 a Nasarawa

Published: 12th, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga da ake zargin makiyaya ne sun kai hari garin Farin Duse da ke Ƙaramar Hukumar Nasarawa, inda suka kashe wata mata juna, Azumi Allah Gaba, tare da wasu mutum 10.

Binciken Aminiya ya nuna cewa rikicin ya samo asali ne lokacin da wani makiyayi ke kiwon shanunsa, ya yanke wata bishiyar mangwaro domin ciyar da dabbobinsa.

Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa

Wani mazaunin yankin ya yi ƙoƙarin hana shi, lamarin da ya haifar da cacar baki a tsakaninsu.

Makiyayin ya harbe mutumin nan take, wanda hakan ya haddasa mummunan rikici tsakanin Fulani makiyaya da manoman Gwari.

Wani ganau da ya buƙaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa: “Rikicin ya fara ne da misalin ƙarfe 6 na safe a ranar Lahadi, 9 ga watan Maris, 2025, har zuwa yammacin Talata.

“Jami’an tsaro sun tabbatar da zaman lafiya, amma har yanzu garin Gwari babu kowa, kuma ana jin harbe-harbe a Farin Ruwa Duse.”

An ƙone gidaje sama da 20 tare da lalata wani ofishin ’yan sanda da ke yankin.

Wasu bayanai sun nuna cewar an lakaɗa wa DPO duka, sannan aka lalata babur ɗinsa.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa, ta tabbatar da mutuwar Azumi Allah Gaba da jaririnta da ke cikinta, tare da wasu mutane.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Nansel Rahman, ya fitar, ya bayyana cewa an kama wasu mutum biyu da ake zargi da hannu a rikicin.

Ya tabbatarwa da jama’a cewa jami’an tsaro sun shawo kan lamarin, kuma ana ci gaba da bincike don kama waɗanda suka aikata laifin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Makiyaya Nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI

Babban zauren MDD ta amince da kudurori guda biyu wadanda suka yi tir da HKI a jiya talata dangane da mamayar da take yiwa kasar Falasdinu tun shekara 1967 da kuma tuddan golan na kasar Siriya.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa HKI ta mamaye tuddan golan na kasar Siriya ne tun yakin kwanaki 6 a shekara 1967 sannan gwamnatin HKI ta tabbatar da kwace yankin a shekara ta 1981. Amma kwamatin tsaron MDD ta yi watsi da mamayar tun lokacin, ta bayyana hakan mamaya ne ba bisa ka’ida ba.

Labarin ya kara da cewa, kasashen Djibouti, Jordan, Mauritania, Qatar, Senegal, da Palestinu ne suka gabatar da kudurin wanda ya sami amincewar kasashe 151, 11 na wadanda basu amince ba (wadanda suka hada da Amurka da HKI) da kuma 11 na wadanda basu kada kuri’arsu ba.

Dangane da tuddan golan kuma wanda kasar Masar ta gabatar, ya sami amincewar kasashe 123, 7 na wadanda basu amince ba sannan 41 na wadanda suka ki kada kuri’unsu. Kudurin da babban zauren ya amince da shi dangane da Falasdinu dai y ana goyon bayan samar da kasashe biyu. Da kuma kira zuwa ga kawo karshen mamayar da HKI take wa kasar Falasdinu tun shekara ta 1967

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Ga Sojojin Ruwa Na Amurka A Kasar Puerto Rico A Shirinta Na Mamayar Venezuela December 3, 2025 Kamfanonin jiragen Sama Na Kasashen Yamma Na Neman Izinin Amurka Don Komawa Iran December 3, 2025 Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI December 3, 2025 An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci December 3, 2025 Nijar ta maka kamfanin hakar uranium na Faransa Orano kotu December 3, 2025 Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10 December 3, 2025 Masar Ta Sanar Da Tattaunawa Da Amurka Don Shirya Sake Gina Gaza December 3, 2025 Isra’ila Ta Hana Motocin Agaji 6000 Shiga Gaza Duk Da Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta December 3, 2025 Kasar Qatar Ta Gargadi Isra’ila Game Da ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza December 3, 2025 Sharhi: HKI tana fama da karancin sojoji a dukkan rassan sojojin kasar December 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAPTIP ta daƙile yunƙurin safarar mutum 7 daga Kano zuwa Saudiyya
  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi
  • Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa
  • ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe
  • MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
  • Wani ya yi shigar mahaifiyarsa da ta mutu ya je karvar kuxin fanshonta
  • Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare
  • An yi garkuwa da manoma 11 a Kudancin Kaduna