Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mai juna biyu da wasu mutum 10 a Nasarawa
Published: 12th, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ake zargin makiyaya ne sun kai hari garin Farin Duse da ke Ƙaramar Hukumar Nasarawa, inda suka kashe wata mata juna, Azumi Allah Gaba, tare da wasu mutum 10.
Binciken Aminiya ya nuna cewa rikicin ya samo asali ne lokacin da wani makiyayi ke kiwon shanunsa, ya yanke wata bishiyar mangwaro domin ciyar da dabbobinsa.
Wani mazaunin yankin ya yi ƙoƙarin hana shi, lamarin da ya haifar da cacar baki a tsakaninsu.
Makiyayin ya harbe mutumin nan take, wanda hakan ya haddasa mummunan rikici tsakanin Fulani makiyaya da manoman Gwari.
Wani ganau da ya buƙaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa: “Rikicin ya fara ne da misalin ƙarfe 6 na safe a ranar Lahadi, 9 ga watan Maris, 2025, har zuwa yammacin Talata.
“Jami’an tsaro sun tabbatar da zaman lafiya, amma har yanzu garin Gwari babu kowa, kuma ana jin harbe-harbe a Farin Ruwa Duse.”
An ƙone gidaje sama da 20 tare da lalata wani ofishin ’yan sanda da ke yankin.
Wasu bayanai sun nuna cewar an lakaɗa wa DPO duka, sannan aka lalata babur ɗinsa.
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa, ta tabbatar da mutuwar Azumi Allah Gaba da jaririnta da ke cikinta, tare da wasu mutane.
A wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Nansel Rahman, ya fitar, ya bayyana cewa an kama wasu mutum biyu da ake zargi da hannu a rikicin.
Ya tabbatarwa da jama’a cewa jami’an tsaro sun shawo kan lamarin, kuma ana ci gaba da bincike don kama waɗanda suka aikata laifin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Makiyaya Nasarawa
এছাড়াও পড়ুন:
An ceto mutane 86 daga hannun ’yan ta’adda 29 a Borno
Rundunar sojin Operation Hadin Kai (OPHK) da ke yaƙi da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas ta sake samun nasara bayan ta ceto mutane 86 da kuma kama wasu mutum 29 da ake zargi da samar wa ’yan ta’adda kayayyaki a Jihar Borno.
A cewar sanarwar da Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar a ranar Litinin, an gudanar da wannan samame ne a ranar 9 ga Nuwamba, bayan samun sahihan bayanan sirri da suka tabbatar da cewa ’yan ta’adda suna garkuwa da fararen hula a kan hanyar Buratai–Kamuya.
Kotu ta sake dakatar da babban taron PDP John Cena ya lashe kambun Intercontinental karon farko a tarihiSojojin Bataliyar Musamman ta 135 da ke ƙarƙashin Sashe na 2 na OPHK sun yi artabu da mayakan Boko Haram da ISWAP a Dutsen Kura, inda suka fatattake su bayan fafatawar da ta gudana har zuwa yankin Mangari.
Sanarwar ta bayyana cewa an gano mafakar ’yan ta’adda guda 11, sannan an kubutar da maza, mata da yara 86 da aka garkuwa da su.
Kayayyakin da aka kwato sun haɗa da bindigar AK-47 guda ɗaya, harsasai 73, jigidar harsashi 5, motoci 5, babura 5, kekuna 8 da kuma babura masu ƙafa uku guda 2.
A wani samame na daban a Mangada, dakarun sun kama mutum 29 da ake zargi da kai wa ’yan ta’adda kayayyaki, tare da kwace motocin ɗaukar kaya guda 2 da babura masu ƙafa uku cike da man fetur da man injin sama da lita 1,000.
Laftanar Kanar Uba ya ce an gudanar da duka ayyukan ba tare da asarar rai ko rauni a ɓangaren sojoji ba, inda babban kwamandan rundunar ya yabawa jarumtar dakarun tare da buƙatar su ci gaba da hana ’yan ta’adda samun damar shakatawa a duk faɗin yankin Arewa maso Gabas.