Aminiya:
2025-12-14@03:19:12 GMT

Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mai juna biyu da wasu mutum 10 a Nasarawa

Published: 12th, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga da ake zargin makiyaya ne sun kai hari garin Farin Duse da ke Ƙaramar Hukumar Nasarawa, inda suka kashe wata mata juna, Azumi Allah Gaba, tare da wasu mutum 10.

Binciken Aminiya ya nuna cewa rikicin ya samo asali ne lokacin da wani makiyayi ke kiwon shanunsa, ya yanke wata bishiyar mangwaro domin ciyar da dabbobinsa.

Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa

Wani mazaunin yankin ya yi ƙoƙarin hana shi, lamarin da ya haifar da cacar baki a tsakaninsu.

Makiyayin ya harbe mutumin nan take, wanda hakan ya haddasa mummunan rikici tsakanin Fulani makiyaya da manoman Gwari.

Wani ganau da ya buƙaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa: “Rikicin ya fara ne da misalin ƙarfe 6 na safe a ranar Lahadi, 9 ga watan Maris, 2025, har zuwa yammacin Talata.

“Jami’an tsaro sun tabbatar da zaman lafiya, amma har yanzu garin Gwari babu kowa, kuma ana jin harbe-harbe a Farin Ruwa Duse.”

An ƙone gidaje sama da 20 tare da lalata wani ofishin ’yan sanda da ke yankin.

Wasu bayanai sun nuna cewar an lakaɗa wa DPO duka, sannan aka lalata babur ɗinsa.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa, ta tabbatar da mutuwar Azumi Allah Gaba da jaririnta da ke cikinta, tare da wasu mutane.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Nansel Rahman, ya fitar, ya bayyana cewa an kama wasu mutum biyu da ake zargi da hannu a rikicin.

Ya tabbatarwa da jama’a cewa jami’an tsaro sun shawo kan lamarin, kuma ana ci gaba da bincike don kama waɗanda suka aikata laifin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Makiyaya Nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

NAFDAC Ta Ƙona Kayayyaki Marasa Inganci Na Naira Biliyan 5 A Nasarawa

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Gwamnatin Nijeriya Ta Himmatu Wajen Inganta Tsarin Karatun Allo December 11, 2025 Manyan Labarai EFCC Ta Kama Tsohon Gwamnan Anambra Chris Ngige A Abuja December 11, 2025 Labarai Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato December 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • EFCC na ƙoƙarin daƙile muradin Malami na yin takarar gwamna — ADC
  • Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno
  • Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota
  • NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa
  • NAFDAC Ta Ƙona Kayayyaki Marasa Inganci Na Naira Biliyan 5 A Nasarawa