Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mai juna biyu da wasu mutum 10 a Nasarawa
Published: 12th, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ake zargin makiyaya ne sun kai hari garin Farin Duse da ke Ƙaramar Hukumar Nasarawa, inda suka kashe wata mata juna, Azumi Allah Gaba, tare da wasu mutum 10.
Binciken Aminiya ya nuna cewa rikicin ya samo asali ne lokacin da wani makiyayi ke kiwon shanunsa, ya yanke wata bishiyar mangwaro domin ciyar da dabbobinsa.
Wani mazaunin yankin ya yi ƙoƙarin hana shi, lamarin da ya haifar da cacar baki a tsakaninsu.
Makiyayin ya harbe mutumin nan take, wanda hakan ya haddasa mummunan rikici tsakanin Fulani makiyaya da manoman Gwari.
Wani ganau da ya buƙaci a sakaya sunansa ya bayyana cewa: “Rikicin ya fara ne da misalin ƙarfe 6 na safe a ranar Lahadi, 9 ga watan Maris, 2025, har zuwa yammacin Talata.
“Jami’an tsaro sun tabbatar da zaman lafiya, amma har yanzu garin Gwari babu kowa, kuma ana jin harbe-harbe a Farin Ruwa Duse.”
An ƙone gidaje sama da 20 tare da lalata wani ofishin ’yan sanda da ke yankin.
Wasu bayanai sun nuna cewar an lakaɗa wa DPO duka, sannan aka lalata babur ɗinsa.
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Nasarawa, ta tabbatar da mutuwar Azumi Allah Gaba da jaririnta da ke cikinta, tare da wasu mutane.
A wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Nansel Rahman, ya fitar, ya bayyana cewa an kama wasu mutum biyu da ake zargi da hannu a rikicin.
Ya tabbatarwa da jama’a cewa jami’an tsaro sun shawo kan lamarin, kuma ana ci gaba da bincike don kama waɗanda suka aikata laifin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Makiyaya Nasarawa
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe
Cibiyar HANs Centre for Social Justice and Development tare da Kanady Academy, sun kammala horon kwana uku domin koya wa yara marasa galihu da matasa mata sana’o’in dogaro da kai a Jihar Gombe.
Shugabar HANs, Barista Hannatu Dauda Simon, ta ce an shirya horon ne domin ƙarfafa gwiwar mahalarta, tare da koya musu yadda za su iya rayuwa ba tare da dogaro da wasu ba.
Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankaliTa ce halin tattalin arziƙin ƙasar nan ya ƙara nuna muhimmancin sana’ar hannu ga matasa.
Ta bayyana cewa matasa mata 100, ciki har da ɗaliban Kanady Academy ne, suka halarci horon.
Masu horarwa daga fannoni daban-daban sun koya wa matasan sana’o’i kamar:
– Yin takalmi
– Yin burodi
– Kwalliya
– Turaren wuta
– Sarrafa kilishi
– Kula da shagunan kaya
– Da sauran sana’o’in dogaro da kai.
Ta yaba da yadda mahalarta suka dage a lokacin horon, tana mai cewa za su yi baje kolin abin da suka koya nan gaba domin nuna ƙwarewarsu.
Ta kuma ce ilimin da aka ba su zai taimaka musu wajen samun abin dogaro da kai.
Wasu daga cikin mahalartan sun bayyana farin cikinsu, inda suka bayyana cewa horon ya taimaka musu gano sana’ar da ta dace da su.
Haka kuma sun yi godiya kan kayan aikin da aka ba su domin su fara ƙananan sana’o’i.