Fiye da Falasdinawa 130 ne Isra’ila ta kashe tun bayan da aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta
Published: 12th, March 2025 GMT
Shugaban ofishin yada labarai a Gaza Salama Marouf, ya yi Allah wadai da ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi, saboda kin janyewa daga yankin Salahul Din a kudancin Gaza da kuma ci gaba da kutsawa da da kai hare-hare a cikin Rafah.
Marouf ya yi gargadin cewa wadannan ayyuka na nuni da irin mummunan nufi da haramtacciyar kasar Isra’ila ke da shi da kuma yadda take ci gaba da aikata laifuffuka kan al’ummar Palasdinu.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Marouf ya bayyana cewa, a cikin kwanaki goman da suka gabata, sojojin Isra’ila sun kara zafafa hare-hare, duk da yarjejeniyar tsagaita bude wuta.
Ya yi nuni da lamari na baya-bayan nan a matsayin shaida na rashin mutunta yarjejeniyar da Isra’ila ta yi, inda ya ba da rahoton cewa an kashe Falasdinawa biyar da suka hada da ‘yan’uwa biyu a kusa da Roundabout na Kuwait a wani harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai a jiya a yankin Rafah.
Wannan laifi dai ya sanya adadin Falasdinawa da aka kashe tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu zuwa mutane 137, inda aka kashe kusan mutane 52 daga cikinsu a Rafah kadai.
Marouf ya yi watsi da ikirarin Isra’ila da ke cewa mayakan Hamas ne ta kaiwa hari, yana mai tabbatar da cewa, a wadannan hare-hare wadanda aka kashe sun sun hada da mata da kananan yara.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita
এছাড়াও পড়ুন:
Rasha ta miƙa wa Ukraine sojoji 1,000 da suka mutu a fagen daga
Rasha ta miƙa wa Ukraine gawarwakin sojoji 1,000 da suka mutu a fagen daga, a cewar wata hukumar gwamnatin Ukraine da ke kula da lamurran fursunonin yaƙi.
Kamfanin Dillancin Labaran Faransa na AFP ya ruwaito cewa ita ma Rashar ta karɓi gawarwakin sojoji 31 daga ɓangaren Ukraine.
Messi ya tsawaita kwantiraginsa da Inter Miami Jami’an tsaro sun kama Sowore saboda shirya zanga-zangaMusayar fursunonin yaƙi da kuma gawarwakin sojoji da suka mutu na daga cikin al’amuran haɗin gwiwa da har yanzu ke gudana tsakanin Kyiv da Moscow, tun bayan mamayar da Rasha ta kai Ukraine a Fabrairun 2022.
Rahotanni daga Kyiv sun ce musayar gawarwakin na daga cikin yarjejeniyar da ɓangarorin biyu suka cimma domin bai wa iyalai damar binne ’yan uwansu cikin mutunci.
“A yau aka gudanar da musayar gawarwaki,” in ji Hedikwatar Tsare-tsaren Ukraine kan Fursunonin Yaƙi a wani saƙo da ta wallafa a shafukan sada zumunta.
Ukraine ta bayyana cewa a musayar da aka yi a lokutan baya, Rasha ta miƙa mata gawarwakin sojojinta yayin da ita ma ke mayar da na ɓangaren Rasha a cikin wani tsarin da ƙungiyar agaji ta Red Cross ke taimakawa wajen sa ido.
A watan Yuli, Agusta da kuma Satumba ne Kyiv ta sanar da karɓar gawarwakin sojoji 1,000 daga Rasha, abin da ke nuna yawan asarar rayuka da ake yi a fagen daga tsakanin ƙasashen biyu.
Hedikwatar ta ce hukumomin tsaro za su fara aikin tantance gawarwakin da aka dawo da su a nan gaba kaɗan, tana mai gode wa Ƙungiyar Red Cross ta Duniya (ICRC) bisa rawar da ta taka wajen tabbatar da nasarar musayar gawarwakin.
A watan Fabrairun bana, Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya shaida wa kafafen yada labaran Amurka cewa ƙasarsa ta rasa sojoji fiye da 46,000, sannan akwai dubbai da ake ɗauka a matsayin wadanda suka ɓata a fagen daga.
Wasu alƙaluma da kafafen labaran BBC da Mediazona suka tattara, sun tabbatar da mutuwar sojojin Rasha sama da 135,000 tun bayan fara yaƙin — duk da cewa sun ce akwai yiwuwar adadin ya zarta haka.