Fiye da Falasdinawa 130 ne Isra’ila ta kashe tun bayan da aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta
Published: 12th, March 2025 GMT
Shugaban ofishin yada labarai a Gaza Salama Marouf, ya yi Allah wadai da ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi, saboda kin janyewa daga yankin Salahul Din a kudancin Gaza da kuma ci gaba da kutsawa da da kai hare-hare a cikin Rafah.
Marouf ya yi gargadin cewa wadannan ayyuka na nuni da irin mummunan nufi da haramtacciyar kasar Isra’ila ke da shi da kuma yadda take ci gaba da aikata laifuffuka kan al’ummar Palasdinu.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Marouf ya bayyana cewa, a cikin kwanaki goman da suka gabata, sojojin Isra’ila sun kara zafafa hare-hare, duk da yarjejeniyar tsagaita bude wuta.
Ya yi nuni da lamari na baya-bayan nan a matsayin shaida na rashin mutunta yarjejeniyar da Isra’ila ta yi, inda ya ba da rahoton cewa an kashe Falasdinawa biyar da suka hada da ‘yan’uwa biyu a kusa da Roundabout na Kuwait a wani harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai a jiya a yankin Rafah.
Wannan laifi dai ya sanya adadin Falasdinawa da aka kashe tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu zuwa mutane 137, inda aka kashe kusan mutane 52 daga cikinsu a Rafah kadai.
Marouf ya yi watsi da ikirarin Isra’ila da ke cewa mayakan Hamas ne ta kaiwa hari, yana mai tabbatar da cewa, a wadannan hare-hare wadanda aka kashe sun sun hada da mata da kananan yara.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya Ta Cimma Sabon Tsarin Hadin Gwiwa Kan Sha’anin Tsaro da Amurka
Daga Bello Wakili
Gwamnatin Tarayya ta ce tattaunawa da tawagarta ta yi da jami’an Amurka ta kara karfafa huldar tsaro tsakanin kasashen biyu tare da bude sabbin hanyoyin hadin gwiwa domin kara kare ‘yan Najeriya.
Tawagar, karkashin jagorancin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, ta gana da manyan jami’an Majalisar Dokokin Amurka, Ofishin Bangaren Addini na Fadar White House, Ma’aikatar Harkokin Waje, Majalisar Tsaro ta Kasa da Ma’aikatar Yaki a birnin Washington DC
A yayin tattaunawar, tawagar ta musanta zargin kisan kare dangi a Najeriya, tana mai jaddada cewa hare-haren da ake samu na shafar al’umma ne daga bangarori daban-daban na kabilu da addinai. Ta ce irin wannan kuskuren fassarar halin da ake ciki na haifar da rarrabuwar kai da kuma karkatar da gaskiyar abin da ke faruwa.
Bayan ganawar, Gwamnatin Amurka ta tabbatar da kudirinta na karfafa huldar tsaro da Najeriya ta hanyar inganta musayar bayanan sirri, hanzarta aiwatar da bukatun kayan aikin tsaro, tare da yiwuwar bayar da karin kayan tsaro na musamman idan sun samu, domin tallafa wa yakin da ake yi da ‘yan ta’adda da kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi.
Amurka ta kuma nuna shirinta na bada tallafin jin kai ga al’ummomin da rikici ya shafa a yankin Arewa ta tsakiya, da kuma taimakawa wajen karfafa tsarin ankararwa da wuri, tare da daukar mataki cikin gaggawa.
Kasashen biyu sun amince da fara aiki kai tsaye da wata yarjejeniyar hadin gwiwa da kafa Kwamitin Aiki na Hada-hadar Tsaro domin tabbatar da tsari guda wajen aiwatar da abin da aka cimma.
A nata bangaren, Najeriya ta sake nanata kudirinta na inganta tsarin kare fararen hula a fadin kasar.
Gwamnatin Tarayya ta ce tattaunawar ta bayar da dama wajen gyara kuskuren fahimta game da halin da ake ciki, ta karfafa amincewar juna, tare da inganta dabarun hadin gwiwa domin kare al’ummomi masu rauni musamman a yankin Arewa ta Tsakiya.
Mambobin tawagar sun hada da Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Prince Lateef Olasunkanmi Fagbemi; Shugaban Hafsoshin Tsaro, Janar Olufemi Oluyede; Daraktan Leken Asiri na Soji, Laftanar Janar Emmanuel Parker Undiandeye; Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Egbetokun; Daraktan Harkokin Ketare a Ofishin mai bai wa Shugaban Kasa shawara kan harkokin tsaro NSA, Ambasada Ibrahim Babani; da Mai Baiwa NSA Shawara ta Musamman, Ms. Idayat Hassan.