Shugaban ofishin yada labarai a Gaza Salama Marouf, ya yi Allah wadai da ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi, saboda kin janyewa daga yankin Salahul Din a kudancin Gaza da kuma ci gaba da kutsawa da da kai hare-hare a cikin Rafah.

Marouf ya yi gargadin cewa wadannan ayyuka na nuni da irin mummunan nufi da haramtacciyar kasar Isra’ila ke da shi da kuma yadda take ci gaba da aikata laifuffuka kan al’ummar Palasdinu.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Marouf ya bayyana cewa, a cikin kwanaki goman da suka gabata, sojojin Isra’ila sun kara zafafa hare-hare,  duk da yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

Ya yi nuni da lamari na baya-bayan nan a matsayin shaida na rashin mutunta yarjejeniyar da Isra’ila ta yi, inda ya ba da rahoton cewa an kashe Falasdinawa biyar da suka hada da ‘yan’uwa biyu a kusa da Roundabout na Kuwait a wani harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai a jiya a yankin  Rafah.

Wannan laifi dai ya sanya adadin Falasdinawa da aka kashe tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu zuwa mutane 137, inda aka kashe kusan mutane 52 daga cikinsu a Rafah kadai.

Marouf ya yi watsi da ikirarin Isra’ila da ke cewa mayakan Hamas ne ta kaiwa hari, yana mai tabbatar da cewa, a  wadannan hare-hare  wadanda aka kashe sun sun hada da mata da kananan yara.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurmin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi

A wata tattaunawa ta wayar tarho da ta gudana tsakanin ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi da takwaransa na kasar masar Badr Abdelatty sun bayyana cewa isra’ila na ci gaba da kai hare-hare da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta a Gaza da kuma kasar labanon,

Ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta mai mataki 20 kan gaza,wanda shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar hujja ce da ta tabbata tun daga farko kamar yadda rahotanni da suka fito daga yankin gaza suka bayyana cewa akalla mutane 366 ne abin ya shafa daga lokacin da aka cimma yarjejeniyar zuwa yanzu.

A watan nuwamba shekara ta 2024 ne aka cimma yarjejeniyar dakatar da bude wuta tsakanin kungiyar hizbulla da HKI bayan hare haren da isra’ila ta kai , da yin kisan kare dangi kan alummar gaza a watan oktoban  shekara ta 2023

An tilastawa Isra’ila  kulla yajejeniyar ce bayan kashi  da ta sha a hannu hizbullah inda ta yi mummuna asara a filin daga, ta kasa cimma burinta bayan kashe mutane fararen hula 400 a kasar labanon.

Haka zalika ministocin harkokin wajen kasashen biyu sun yi musayar ra’ayi game da dangantar dake tsakaninsu kuma sun amince a ci gaba da tattaunawa sosai kan yadda za su kara fadada dangantakar dake tsakani

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka   Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba December 6, 2025 Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika December 6, 2025 Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi December 6, 2025 Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026 December 6, 2025 Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza December 6, 2025 Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta December 6, 2025 Rasha Tace Ta Kakkabo Jiragen Drones Na Ukrai 116 A Daren Jiya December 6, 2025 ‘Yar Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya na wasan harbi a karo na 4 December 6, 2025 Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyi 20 da kwangiloli 5 a fannin fasaha December 6, 2025 Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’
  • Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila
  • Masar : ba za mu bari a yi amfani da iyakar Rafah ba don korar Falasdinawa
  • Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi
  • Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurmin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi
  •   Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba
  • Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi
  • Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta
  • Na’im Kassim Ya Yi Suka Akan Shigar Kasar Cikin Kwamitin Tattaunawa Da “Isra’ila” Kai Tsaye
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe