Shugaban ofishin yada labarai a Gaza Salama Marouf, ya yi Allah wadai da ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi, saboda kin janyewa daga yankin Salahul Din a kudancin Gaza da kuma ci gaba da kutsawa da da kai hare-hare a cikin Rafah.

Marouf ya yi gargadin cewa wadannan ayyuka na nuni da irin mummunan nufi da haramtacciyar kasar Isra’ila ke da shi da kuma yadda take ci gaba da aikata laifuffuka kan al’ummar Palasdinu.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Marouf ya bayyana cewa, a cikin kwanaki goman da suka gabata, sojojin Isra’ila sun kara zafafa hare-hare,  duk da yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

Ya yi nuni da lamari na baya-bayan nan a matsayin shaida na rashin mutunta yarjejeniyar da Isra’ila ta yi, inda ya ba da rahoton cewa an kashe Falasdinawa biyar da suka hada da ‘yan’uwa biyu a kusa da Roundabout na Kuwait a wani harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai a jiya a yankin  Rafah.

Wannan laifi dai ya sanya adadin Falasdinawa da aka kashe tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu zuwa mutane 137, inda aka kashe kusan mutane 52 daga cikinsu a Rafah kadai.

Marouf ya yi watsi da ikirarin Isra’ila da ke cewa mayakan Hamas ne ta kaiwa hari, yana mai tabbatar da cewa, a  wadannan hare-hare  wadanda aka kashe sun sun hada da mata da kananan yara.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita

এছাড়াও পড়ুন:

Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas

Mutum uku da wani yaron babbar motar kaya sun rasa ransu bayan wayar wutar lantarki kashe su a lokacin wani bikin nadin sarauta a unguwar Idimu da ke Ƙaramar Hukumar Alimosho ta jihar Legas,

bayanai sun nuna cewa lamarin ya faru ne ranar Talata, 11 ga watan Nuwamba, kuma an gano cewa yaron motar, wanda ba a tantance sunansa ba tukuna, ya mutu nan take a wurin.

Najeriya ta ɗora alhakin taɓarɓarewar harkokin tsaronta kan Amurka Babu addinin da ake yi wa kisan ƙare dangi a Binuwai — Gwamna Alia

Rahotanni sun ce wani mazaunin unguwar da aka karrama da sarauta ne ya shirya taron cashiyar a titin Anjorin domin murnar nadin.

Sai dai yayin da ake tsaka da bikin, wata babbar mota mai ɗaukar yashi ta yi ƙoƙarin shiga layin amma ta samu cikas saboda ɗaya daga cikin tantunan da aka kafa a kan hanya.

Wani ganau mai suna Femi Ajiboye, ya shaida wa wakilinmu a ranar Laraba cewa yayin da suke ƙoƙarin matsar da tantin gefe, ƙarfen tantin ya taɓa wayar lantarki, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar su nan take.

Femi ya ce, “Bikin nadin sarauta ya ɗauki mako guda ana yin sa, kuma a cikin wannan lokaci wani mazaunin unguwar ya sami sarauta. Yayin da yake gudanar da wani taro na musamman don murnar nadin, wata mota mai ɗaukar yashi ta yi ƙoƙarin shiga sabon rukunin gidajen da ke ƙarshen titin, amma tantin da aka kafa ya tare hanya.
“A lokacin ne wasu daga cikin mahalarta bikin tare da ɗaya daga cikin yaran motar suka ɗage tantin daga hanya.

“Ba tare da sun ankara ba, ashe akwai budaddiyar wayar lantarki a ƙasa. Da ƙarfen tantin ya taɓa wayar, sai wutar ta ja su. Mutane ba su fahimci abin da ke faruwa ba sai da suka ga sun faɗi a ƙasa. A lokacin ne aka gane cewa wutar lantarki ce ta kashe su,” in ji Femi.

Rahotanni sun ce lamarin ya jefa taron cikin alhini, inda aka dakatar da bukin nan take.

Wani mazaunin unguwar da ya bayyana sunansa da Olajide, ya ce an garzaya da waɗanda abin ya shafa zuwa asibiti, inda aka tabbatar da mutuwar yaron motar nan take.

“Dukkan yankin ya rikice lokacin da lamarin ya faru saboda mutane sun yi tunanin sun mutu gaba ɗaya. An kai su huɗun asibiti, amma yaron motar bai tsira ba. Sauran baƙi uku an karɓe su kuma suna samun kulawa a yanzu,” in ji shi.

Olajide ya ƙara da cewa iyalan mamacin sun ɗauki gawarsa daga baya suka yi masa jana’iza.

Wani mazaunin unguwar da ya nemi a ɓoye sunansa saboda dalilai na sirri ya ce ya ga mamacin kafin lamarin, lokacin da ya sayi dizal a gidan mai.

“Na ga mutumin lokacin da ya sayi dizal a tashar mai ba da jimawa ba. Na yi matuƙar mamaki da aka ce ya mutu. Wannan mutumin da na gani kimanin mintuna talatin kafin haka,” in ji shi.

Lokacin da aka tuntubi jami’an ‘yan sanda a ranar Lahadi don jin ta bakinsu, jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sandan jihar ta ce ba ta da masaniya.

Ta ce: “Na kira DPO na yankin, ta ce babu irin wannan rahoto da aka kawo ofishin ’yan sanda.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Yarjejeniyar  Da Aka Cimma Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA A Kasar Masar Ta Rushe
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Kiran Da A Sanya Isra’ila Cikin Jerin Masu Aikata Abin Kunya Saboda Kashe Yara
  • Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas
  • Hamas Tayi Gargadi Game Da Kara Dagulewar Al’amura Bayan Harin Isra’ila A Gaza
  • Labanon Ta Bukaci Gudanar Da Taron Kwamitin Tsaro Na MDD Cikin Gaggawa
  • Isra’ila ta kashe akalla Falasdinawa 27 a wani sabon harin bam
  • Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta A Gaza Kusan Sau 400
  • Kimanin Falasdinawa 2 Ne Suka yi Shahada Sakamakon Harin Isra’ila  A  Ainul Hilwa
  • Gobara ta laƙume kasuwar Katako a Gombe
  • Harin Isra’ila ya kashe mutum 15 a sansanin ‘yan gugun hijira na Falasdinawa a Lebanon