Shugaban ofishin yada labarai a Gaza Salama Marouf, ya yi Allah wadai da ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi, saboda kin janyewa daga yankin Salahul Din a kudancin Gaza da kuma ci gaba da kutsawa da da kai hare-hare a cikin Rafah.

Marouf ya yi gargadin cewa wadannan ayyuka na nuni da irin mummunan nufi da haramtacciyar kasar Isra’ila ke da shi da kuma yadda take ci gaba da aikata laifuffuka kan al’ummar Palasdinu.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Marouf ya bayyana cewa, a cikin kwanaki goman da suka gabata, sojojin Isra’ila sun kara zafafa hare-hare,  duk da yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

Ya yi nuni da lamari na baya-bayan nan a matsayin shaida na rashin mutunta yarjejeniyar da Isra’ila ta yi, inda ya ba da rahoton cewa an kashe Falasdinawa biyar da suka hada da ‘yan’uwa biyu a kusa da Roundabout na Kuwait a wani harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai a jiya a yankin  Rafah.

Wannan laifi dai ya sanya adadin Falasdinawa da aka kashe tun bayan da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu zuwa mutane 137, inda aka kashe kusan mutane 52 daga cikinsu a Rafah kadai.

Marouf ya yi watsi da ikirarin Isra’ila da ke cewa mayakan Hamas ne ta kaiwa hari, yana mai tabbatar da cewa, a  wadannan hare-hare  wadanda aka kashe sun sun hada da mata da kananan yara.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta laƙume kasuwar Katako a Gombe

Wata mummunar gobara ta tashi cikin daren Laraba ta ƙone shaguna a kasuwar Katako da ke Gombe, lamarin da ya yi sanadin salwantar dukiya ta miliyoyin naira.

Shaidu sun ce gobarar ta fara ne wajen misalin ƙarfe 1:00 na dare sakamakon zargin matsalar wutar lantarki, inda ake kyautata zato cewa an bar wasu na’urorin lantarki ne a kunne bayan an rufe kasuwar.

DAGA LARABA: Hanyoyin Da Suka Kamata A Bi Wajen Ceto Daliban Kebbi Da Aka Sace Amurka za ta binciki zargin yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya ranar Alhamis

Hakan a cewar shaidun ya haddasa tashin gobarar bayan wutar lantarki ta dawo.

Gobarar dai ta ci gaba da ƙone shaguna da kadarori iri-iri, lamarin da ya jefa ’yan kasuwa cikin damuwa da alhini.

Kasuwar Katako na daga cikin manyan cibiyoyin hada-hadar kasuwanci a jihar wacce jigo ce wajen samar wa dubban mazauna Gombe kudaden shiga.

Jami’an hukumar kashe gobara sun shiga aikin ceto da wuri domin dakile bazuwar wutar, sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, ba a tantance adadin shagunan da suka ƙone ko jimillar asarar da aka yi ba.

Muna tafe da karin bayani…

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta kashe akalla Falasdinawa 27 a wani sabon harin bam
  • Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta A Gaza Kusan Sau 400
  • Kimanin Falasdinawa 2 Ne Suka yi Shahada Sakamakon Harin Isra’ila  A  Ainul Hilwa
  • Gobara ta laƙume kasuwar Katako a Gombe
  • Harin Isra’ila ya kashe mutum 15 a sansanin ‘yan gugun hijira na Falasdinawa a Lebanon
  • GGCSS Maga: Halin da iyaye ke ciki bayan sace ’ya’yansu
  • Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi
  • Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a Borno
  • ‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
  • Sojojin HKi Sun Kashe Wasu Falasdinawa Guda 2 A Sansanin Yan Gudun Hijira