HausaTv:
2025-10-20@21:08:12 GMT

EU ta jadadda bukatar warware batun Iran ta hanyar diflomasiyya

Published: 12th, March 2025 GMT

Kungiyar tarayyar turai ta jaddada bukatar warware batun Iran ta hanyar diflomatsiyya.

Da taek sanar da hakan babbar Jami’ar kula da harkokin ketare ta kungiyar ta ce babu wata hanyar da za’a bi wajen warware matsalar Iran in ba ta diflomasiyya ba.

‘’ta hanyar diflomatsiyya ne za’a warware takaddamar da ake game da batun yarjejeniyar nukiliyar da aka cimma a shekarar 2015 da iran, inji Kaja Kalas.

Da take magana a taron shekara-shekara na kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya kan hadin gwiwa tsakanin EU da Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York, babbar jami’ar ta Tarayyar Turai ta ce “ci gaba da fadada shirin nukiliyar Iran ya sabawa alkawurran da Iran ta dauka kamar yadda kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da shi.

“A lokaci guda kuma, hanyar da ta shafi bangarori daban-daban, kamar yarjejeniyar, tana da mahimmanci.

Ta ce, “Babu wata hanyar da za ta dore wajen warware matsalar sai ta diflomasiyya,” in ji ta, a cewar shafin yanar gizon EU External Action.

A kwanan ne dai shugaban AMurka Donald Trump, y ace ya aike da wasiga ga Iran, na ta bude tattaunwa ko kuma ya yi da karfin soji.

Iran dai ta musanya samun wata wasika daga Trump, kuma tana mai cewa babu batun tattaunawa bsia matsin lamba da barazana.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

 

Gwamnan ya kuma buƙaci mambobin majalisar da su kasance masu aiki da faɗakarwa, su kasance kusa da jama’ar yankunansu da kuma shugabannin ƙananan hukumomi. Ya umarce su da su riƙa isar da rahotanni na yau da kullum ga Kwamishinan Tsaro, tare da yin addu’a ga waɗanda suka rasa rayukansu wajen kare al’umma da zaunar da zaman lafiya a jihar.

 

Bugu da ƙari, Gwamna Lawal ya ƙarfafa mambobin majalisar su ƙara haɗin kai da sauran jami’an gwamnati domin tabbatar da ingantacciyar tafiyar da al’amuran mulki da gudanar da ayyukan ci gaba cikin nasara.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta October 20, 2025 Ra'ayi Riga Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa October 20, 2025 Manyan Labarai Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a October 20, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Karbi Bakwancin Takwaransa Na Iraki
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro
  • Grossi: Za a iya warware batun Shirin nukiliyar Iran ne kawai ta hanyar diflomasiyya
  • Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Bayyana Cewa: Kuduri Mai Lamba 2231 Ya Zo Karshe
  • Jami’in Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce: An Rusa Gaza Gaba Daya
  • Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU
  •  Majalisar Dattawa Za Ta Gana Da Ministan Ilimi Kan Batun Yajin Aikin Asuu.
  • Iran: Kauyuka Guda Uku Na Kasar Sun Shiga Cikin Kauyukan Yawon Shakatawa Ta Duniya
  • Kwamandan Rundunar Kudancin Amurka ya sanar da murabus kan  batun  ayyukan soji a yankin Caribbean