Leadership News Hausa:
2025-09-18@00:53:58 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [4]

Published: 12th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [4]

Wannan umurni yana da tushen shari’a daga Alƙur’ani da Hadisi, kuma yana da hikima da fa’ida da dama. Allah Ta’ala Ya umurci Musulumi da yin isti’aza kafin karanta Alƙur’ani kamar yadda Ya labarta mana haka a cikin Suratul Nahli a aya ta 98. Inda Ya ce:” To idan za ka karanta Alƙur’ani sai ka nemi tsarin Allah daga Shaiɗan korarre (daga rahamar Allah).

” Wannan aya ta tabbatar da neman tsarin Allah kafin a fara karatun Alƙur’ani.

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [1] CIYARWA [Falalarta Da Muhimmancinta] Na 1

Ma’anar Isti’aza:

Isti’aza na nufin neman tsari da kariya da fake wa a wurin Allah Shi kaɗai ban da waninsa daga sharrin Shaiɗan. Domin ƙarin haske duba Ibnu Jarir; Jãmi’ul Bayãni [1/111], Ibnu Kasir; Tafsirul Kur’anil Azim [1/27], da Ibnul Ƙayyim; Badã’i’ul Fawã’id [2/200].

Yaushe ake Isti‘aza?:
Malamai sun yi saɓani dangane da lokacinda za a yi Isti‘aza, sai dai magana mafi ingani da malamai mafiya yawa suke a kanta shi ne ana yin Isti‘aza ne kafin a fara karatu. Domin ƙarin haske duba Ibnu Ibnu Juzai; Kitãbut Tashīl fi Ulūmil Kitãbi [1/30], da Bagawī; Ma’ãlumut Tanzīli [[5/42] da Ibnu Aɗiyya; al-Muharrul Wajizi [1/58], da Ibnul Jauzi; Zãdul Masīri [1/14].

Hukunci Isti‘aza Kafin Karanta Alƙur’ani:

Malamai mafiya yawa sun tafi a kan mustahabbi ne yin isti‘aza a lokacin karanta Alƙur’ani a wajen salla. Amma sun yi saɓani a wajen karatun salla, an hakaitu Imamu Malik ba ya isti‘aza a sallar farilla amma yana yi a sallar asham, shi sa ake yi a sallar nafila. Amma Imam Abu Hanifa da Imam Asshafi’i suna yi isti‘aza a sallar farilla. Akwai waɗanda suke ganin wajibi ne a yi isti‘aza a salla gaba ɗaya. Domin ƙarin haske duba Kitãbu at-Tashīlu fi Ulūmi at-Tanzil [1/30] da Ibnu Kasir; Tafsirul Kur’anil Azim [1/26] da al-Ƙurɗubi; al-Jãmi’u Li’ahkãmil Ƙur’ãni [1/86]

Hikimar Yin Isti’aza Kafin Karanta Alƙur’ani:

Akwai hikimomi masu tarin yaw na yin isti‘aza kafin karatu. Ga wasu daga cikinsu:

1. Kariya daga tasirin Shaiɗan: Shaiɗan yana hana mutum fahimtar Alƙur’ani kuma yana kuma sanya ruɗani. Yin isti’aza na kare mai karatu daga fitinarsa.

2. Tsaftace zuciya: Isti’aza kafin karanta karanta Alƙur’ani yana ba wa zuciya tsarki da nufin Allah a karatu da samin tsoron Allah, tare da tadabburi.

3. Bin sunnon Annabi (SAW): Domin Annabi (SAW) yana Isti’aza kafin ya fara karatu.

4. Tsaftace Baki: Yin isti‘aza yana tsaftace baki daga abuwan da ta aikata na wargi da yasasshen zance, domin shiga karanta maganar Allah cikin tsarki da tsafta.

Daga: Abu Razina, Nuhu Ubale Paki

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan isti aza kafin karanta Isti aza kafin karanta karanta Alƙur ani

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato

Gwamnan Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, ya ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani guda 20, tare da riguna ruwa (life jackets) 2,000, domin rage haɗurran da ke aukuwa sakamakon ambaliya da nutsewar jirage a sassan jihar.

An ƙaddamar da jiragen ne a ƙaramar hukumar Wamakko a ranar Laraba, inda gwamnan ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin shirin gaggawa na tallafa wa al’ummar da ke fama da illar ambaliya da haɗurra a ruwa.

Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB

“Mun dauki wannan mataki bayan rahotannin da muke samu na yawaitar hatsarurruka da rasa rayuka da dukiya sakamakon jiragen katako da mutane ke amfani da su,” in ji Gwamna Ahmad Aliyu.

Gwamnan ya miƙa godiya ga shugabar hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), Hajiya Zubaida Umar, bisa hadin kai da goyon bayan da hukumar ke bayarwa domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiya, tare da inganta ayyukan ceto da agaji a jihar.

Aminiya ta ruwaito cewa, an horar da direbobin jiragen ruwan da za su riƙa kula da su, kafin a raba su zuwa ƙananan hukumomi goma (10) da suka fi fuskantar barazanar ambaliya da suka haɗa da: Goronyo, Shagari, Sabon-Birni, Wurno, Rabah, Wamakko, Silame, Kebbe, Tambuwal da Isa.

Gwamnan ya kuma yi gargaɗin cewa za a hukunta duk wani da ya ɗauki lodi fiye da ƙima a cikin jiragen, yana mai cewa “wannan jirage da rigar ruwa na jama’a ne, kuma wajibi ne shugabannin ƙananan hukumomi su tabbatar da kula da su yadda ya kamata.”

Sai dai wasu daga cikin mazauna yankunan da za a rabawa jiragen sun bayyana ra’ayinsu dangane da lamarin, inda wani Tanimu Goronyo, daga karamar hukumar Goronyo, ya ce: “Gwamnatin Sakkwato ta kauce hanya.

“Abin da muke bukata a yanzu shi ne hanyoyin mota da magudanan ruwa. Ambaliya tana mamaye yankunan mu ne saboda babu hanya. Idan gwamnati ta kashe wannan kuɗi wajen gina hanya, sai an fi cin moriya.”

Shi ma wani Muhammad Kabiru, daga Silame, ya bayyana farin cikinsa da sayen jiragen, sai dai ya roƙi gwamnati da ta mai da hankali wajen gina hanyoyin mota saboda abin da suka fi buƙata ke nan.

“Mu a Silame jirgi yana da amfani, amma hanyar mota ita ce babbar buƙatar mu. Idan aka samar da ita, ambaliya ba za ta hana mu zirga-zirga ba.”

Yayin da gwamnatin Sakkwato ke ɗaukar matakan gaggawa don rage hatsarurruka da ambaliya ke haifarwa, al’umma na ci gaba da neman tsarin da zai magance tushen matsalar – musamman samar da ingantattun hanyoyi da magudanan ruwa a karkara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki