Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Kidayar Jama’a Na Kasa
Published: 17th, April 2025 GMT
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kaddamar da wani babban kwamiti kan kidayar jama’a da gidaje mai zuwa, inda ya umurci mambobin su gabatar da rahoton farko cikin makonni uku.
Shugaban wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan fadar sa, Femi Gbajabiamila, a wajen taron da aka gudanar a fadar gwamnati da ke Abuja, ya ce kidayar na da matukar muhimmanci ga ci gaban kasa da kuma tsare-tsare na gaskiya.
Ya lura cewa ingantaccen bayanan yawan jama’a yana da mahimmanci don yanke shawara mai inganci a cikin manyan sassan kamar kiwon lafiya, ilimi, tsaro, da kuma tsara tattalin arziki.
Shugaban ya jaddada cewa, an gudanar da kidayar jama’a ta karshe a shekarar 2006, wato kusan shekaru ashirin da suka wuce, kuma tun daga lokacin ne Najeriya ta fuskanci sauye-sauye a yawan al’umma, matsugunan jama’a, da kuma muhimman abubuwan da suka shafi kasa baki daya.
Ya kuma jaddada mahimmancin tsarin da aka yi amfani da shi na fasaha don tabbatar da sahihin sakamako mai inganci, inda ya bayyana bukatar yin hadin gwiwa a tsakanin dukkanin hukumomin da abin ya shafa, da suka hada da hukumar kidaya ta kasa, da hukumar kula da shaida ta kasa NIMC, da ma’aikatar kudi, da ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsare.
Shugaban kwamitin shugaban kasa kan kidayar jama’a da gidaje kuma ministan kasafin kudi da tsare-tsare, Sanata Atiku Bagudu, ya tabbatar da cewa kwamitin zai gabatar da rahotonsa cikin wa’adin makonni uku da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar.
Bello Wakili/Abuja
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwamiti kidayar jama a
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a yi koyi daga akidun dan mazan jiya, kuma jagora na gari Chen Yun, tare da kara azamar dorar da kyawawan dabi’unsa cikin himma da kwazo, don gina kasar Sin mai matukar karfi.
Shugaba Xi, wanda shi ne babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban hukumar koli ta rundunar sojojin kasar, ya yi kiran ne a yau Juma’a, cikin jawabin da ya gabatar, yayin taron bikin murnar cika shekaru 120 da haihuwar Chen Yun, taron da ya gudana a babban dakin taruwar jama’a dake tsakiyar birnin Beijing
Shugaban na Sin ya ce, an haifi Chen a shekarar 1905, ya kuma shiga JKS a shekarar 1925. Ya kuma kasance shahararren dan gwagwarmaya a rundunar ‘yantar da al’umma kuma dattijon arziki, kana daya daga cikin kusoshin da suka kafa tsarin tattalin arziki na gurguzu na kasar Sin. Kazalika, ya kasance muhimmin memba cikin jerin shugabannin JKS zangon farko mai Mao Zedong a matsayin babban jigo, kana da shugabannin JKS zango na biyu mai Deng Xiaoping a matsayin babban jigo. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp