Jami’an hukumar shiyyar Kaduna na hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, sun kama wasu mutane arba’in da ake zargi da damfarar yanar gizo a kananan hukumomin Bida da Minna na jihar Neja.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban hukumar EFCC, Dele Oyewale ya raba wa manema labarai a Minna babban birnin jihar Neja.

 

A cewarsa an kama su ne biyo bayan sahihan bayanan sirri da ke alakanta su da ayyukan damfara na intanet.

 

Kayayyakin da aka kwato daga hannunsu sun hada da motoci uku, na’urorin samar da wutar lantarki guda takwas, na’urar sanyaya daki samfurin Hisense guda daya, na’urorin sarrafa wutar lantarki guda biyu, babura 10, kwamfutocin tafi da gidanka guda takwas, na’urar magana ta bluetooth hudu da wayoyin android 60 da dai sauran kayyaki.

 

Za a gurfanar da wadanda ake zargin zuwa kotu da zarar an kammala bincike.

 

PR ALIYU LAWAL.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da naɗa Muhammad Fa’iz a matsayin Kwamanda Janar na farko na Hukumar Hisbah ta Jihar.

Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ne ya tabbatar da naɗin ga manema labarai a Dutse.

Ya bayyana cewa hakan na daga cikin ƙoƙarin Gwamna Namadi na ƙarfafa ayyukan sabuwar hukumar Hisbah da inganta aikinta.

A cewar sa, naɗin ya haɗa da Dr. Husaini Yusuf Baban a matsayin Babban Mataimakin Kwamanda Janar, da Lawan Danbala a matsayin Mataimakin Kwamanda Janar da hedikwatar hukumar, da kuma Yunusa Idris Barau a matsayin Mataimakin Kwamanda Janar naYankin Dutse.

Sauran su ne Abdulkadir Zakar, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Hadejia, da Suraja Adamu, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Gumel, da Bello Musa Gada, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Kazaure, sai  Barrister Mustapha Habu a matsayin Sakatari kuma Lauya mai ba da shawara.

Malam Bala Ibrahim ya jaddada cewa an zaɓi waɗannan mutane ne bisa cancanta, ƙwarewa da kuma nagartar halayensu, yana mai kira gare su da su yi kokarin sauke nauyin da aka dora musu.

Sakataren Gwamnatin Jihar  ya ce an riga an mika musu takardun naɗi kuma sun shirya tsaf don fara aiki nan take.

A nasa bangaren, Muhammad Fa’iz ya gode wa Gwamna bisa amincewar da ya nuna musu, tare da alƙawarin gudanar da aiki da ƙwazo da himma.

 

 

Usman Muhammad Zaria 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom
  • An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja