Hadin Gwiwar Kasashen Asiya Da Afirka Na Habaka Karfinsu Na Dogaro Da Kai Da Cin Moriya Tare
Published: 17th, April 2025 GMT
Wato na farko, dogaro da kai a bangare makamashi, shawarar “ziri daya da hanya daya” ta kafa wani tsarin tattalin arziki dake amfanar da dukkan kasashen Asiya da Afirka, sun kuma kara karfin kafa tsare-tsaren samar da kayayyaki na mabambantan bangarori a shiyyar ta hanyar kara tuntuba, da dunkulewar manyan ababen more rayuwa, da yin musayar fasahohi, wanda hakan ya sa kasashen ba sa dogaro da sana’ar fitar da makamashi kawai, matakin da ya kara musu kwarin gwiwar samun bunkasuwa da kansu.
Na biyu, samun jari da kansu. Sabon bankin raya mambobin BRICS, da bankin zuba jari na Asiya da dai sauran hukumomi, sun baiwa kasashe masu tasowa wata hanyar samun jari na daban ban da kasashen yamma. Ya zuwa shekarar 2025, bankin zuba jari na Asiya ya amince da ba da rancen kudi da yawansu ya kai dalar biliyan 44.7, an zuba kashi 58% daga cikinsu a kasashe ko yankuna marasa ci gaba a bangaren kafa manyan ababen more rayuwa, ta yadda ba sai sun dogara da IMF da sauran hukumomi irinsa su kadai ba.
Na uku, daidaita manufofin cinikin duniya. Hadin gwiwar ciniki cikin ’yanci na Afirka da RCEP, ya rarraba aikin samar da kayayyaki ga bangarori daban-daban, kuma hakan ya gaggauta raguwar harajin kwastam tsakanin kasashe da batun ya shafa da kashi 37%. Kazalika, ya kawar da matsin lamba, da barazana da kasashe wasu wadata ke haifarwa kasashe masu tasowa ta amfani da shingayen ciniki. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkiya ya bayyana cewa dukkan kasashe mambobia a kungiyar ECO ta raya tattalin arziki na kasashen yankin sun yi tir da HKI a taron kungiyar wanda aka gudanar a birnin Khankendi. Na kasar Azerbaijan. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto shugaban yana fadar haka bayan tawowarsa daga taron a daren jumma’a a kuma shafinsa na X. Shugaban ya kuma kara da cewa Tehran a shirye take ta hada kai da wadannan kasashe makobta don taimakawwa juna a dukkan bangarorin rayuwa wadanda suka hada da kyautata tattalin arzikin yankin da al-adu da sauransu.
Shugaban ya bayyana cewa yana godiya ga dukkan kasashen kungiyar ECO da kuma sauran kasashen yankin da sauran kasashen duniya wadanda suka nuna goyon bayansu ga kasarsa bayan yakin kwanaki 12 da HKI da kuma Amurka.
Daga karshe yace yana fatan kasar da sauran kasashen kungiyar ECO zasu kai ga gurunsu na bunkasar tattalin arziki ta shekara ta 2035.
A ranar jumma’a 13 ga watan Yuni ne jiragen yakin HKI suka kai hare-hare a kan Iran inda suka kashe manya-manyan jami’an sojojin kasar da masana fasahar Nukliya da kuma fararen hula wadanda basu san hawa ko sauka ba. Sannan Amurka ta kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar da suke fordo Natanz da kuma Esfahan.