Hadin Gwiwar Kasashen Asiya Da Afirka Na Habaka Karfinsu Na Dogaro Da Kai Da Cin Moriya Tare
Published: 17th, April 2025 GMT
Wato na farko, dogaro da kai a bangare makamashi, shawarar “ziri daya da hanya daya” ta kafa wani tsarin tattalin arziki dake amfanar da dukkan kasashen Asiya da Afirka, sun kuma kara karfin kafa tsare-tsaren samar da kayayyaki na mabambantan bangarori a shiyyar ta hanyar kara tuntuba, da dunkulewar manyan ababen more rayuwa, da yin musayar fasahohi, wanda hakan ya sa kasashen ba sa dogaro da sana’ar fitar da makamashi kawai, matakin da ya kara musu kwarin gwiwar samun bunkasuwa da kansu.
Na biyu, samun jari da kansu. Sabon bankin raya mambobin BRICS, da bankin zuba jari na Asiya da dai sauran hukumomi, sun baiwa kasashe masu tasowa wata hanyar samun jari na daban ban da kasashen yamma. Ya zuwa shekarar 2025, bankin zuba jari na Asiya ya amince da ba da rancen kudi da yawansu ya kai dalar biliyan 44.7, an zuba kashi 58% daga cikinsu a kasashe ko yankuna marasa ci gaba a bangaren kafa manyan ababen more rayuwa, ta yadda ba sai sun dogara da IMF da sauran hukumomi irinsa su kadai ba.
Na uku, daidaita manufofin cinikin duniya. Hadin gwiwar ciniki cikin ’yanci na Afirka da RCEP, ya rarraba aikin samar da kayayyaki ga bangarori daban-daban, kuma hakan ya gaggauta raguwar harajin kwastam tsakanin kasashe da batun ya shafa da kashi 37%. Kazalika, ya kawar da matsin lamba, da barazana da kasashe wasu wadata ke haifarwa kasashe masu tasowa ta amfani da shingayen ciniki. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
Da yake magana kan muhimmancin bikin Ranar Dimokiraɗiyya ta bana, Idris ya ce wannan ba lokacin murna kaɗai ba ne, har ma lokaci ne na nazari kan cigaban ƙasar wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya da farfaɗowar tattalin arziki.
Ya bayyana cewa ana amfani da kuɗaɗen da aka tara daga cire tallafin man fetur wajen gina muhimman ababen more rayuwa, ciki har da manyan tituna guda biyu da za su haura kilomita 1,700, waɗanda za su taimaka wajen bunƙasa harkokin kasuwanci da haɗa yankuna daban-daban.
Ya ce: “Manufar ba wai haɗa yankuna ba ce kawai, amma samar da damarmakin tattalin arziki.
“Nijeriya na ƙoƙarin komawa kan sahihiyar hanyar ta. Tana sake zama ƙasa mai daraja a idon duniya.
“Martabar da Nijeriya ke da ita a baya tana dawowa sannu a hankali. Masu zuba jari suna samun ƙarin ƙwarin gwiwa a ƙasar.”
Ya ƙara da cewa sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa ƙarƙashin Shirin Sabunta Fata sun wuce batun tattalin arziki kawai, domin suna gina tushe ne na cigaba mai ɗorewa, raba dama ga kowa, da ƙarfafa gaskiya da riƙon amana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp