Leadership News Hausa:
2025-05-21@21:14:47 GMT

Yaukaka Zumunci Da Makwabta A Aikace Tsakanin Sin Da Malaysiya

Published: 16th, April 2025 GMT

Yaukaka Zumunci Da Makwabta A Aikace Tsakanin Sin Da Malaysiya

Kasar Sin ta kuma nuna aniyarta ta lale marhabin ga shigar da karin kayan amfanin gona masu inganci na Malaysiya zuwa katafariyar kasuwarta inda ta kuma nemi kasar ta Malaysiya ta kara bai wa kamfanoninta kwarin gwiwar zuba jari a kasar.

 

Kasar Malaysiya ta san irin alheran da kamfanonin Sin suke ci gaba da kawo mata wajen raya tattalin arziki da ci gaban masana’antunta.

Wannan ya sa Sultan Ibrahim ya bayyana cewa, Malaysiya tana dora fifiko sosai a kan zumuncinta da kasar Sin, kuma za su ci gaba da yin aiki tare domin samun nasara ga kowane bangare, tare da kara matsa kaimi ga gina al’umma mai makoma ta bai-daya a karkashin ingantattun manyan tsare-tsare kuma a duk wani sauyi da za a iya samu a duniya.

 

Tabbas, Malaysiya tana shaida irin ci gaban da kamfanonin kasar Sin suke kawo mata. Babban jami’in kasuwanci na tashar teku ta Kuantan, Mazlim Husin, ya bayyana yadda yankin masana’antu na hadin gwiwar Sin da Malaysiya (MCKIP) ya bude sabon babi ga bunkasa ci gaban Kuantan tun bayan kaddamar da shi a shekarar 2013. Kafa kamfanin mulmula karafa na Alliance Steel ya kara wa sauran kamfanoni kwarin gwiwar bude rassansu a yankin masana’antun wanda ya habaka samar da ayyukan yi da walwalar al’ummar wurin.

 

Kasar Sin ta kasance kasar da ta fi kowace kasa zuba jari a Malaysiya, inda ko a bara ta zuba kimanin dala biliyan 6.4 a kasar wanda ya kai kaso 16 na kudin shigar da Malaysiya ke samu daga zuba jarin kasashen waje kuma ana sa ran ya samar da sabbin guraben ayyukan yi 20,000.

 

Kazalika, wani jami’in ofishin jakadancin Malaysiya mai kula da zuba jari dake Guangzhou, Safwan Nizar Johari ya tabbatar da cewa akwai karin kamfanonin Sin dake zuba jari a kasar musamman a bangaren motocin sabbin makamashi, wanda hakan na nuna zumunci mai kyau tsakanin Sin da makwabtanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Malaysiya ta a Malaysiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kano Za Ta Yaki Cutar Hawan Jini Tare Da Hadin Gwiwar Kungiyar Global Effort

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano ta ce ta samu gagarumar nasara wajen shiga sahun kasashen duniya a ranar cutar hawan jini ta duniya.

Kwamishinan lafiya Dr Abubakar Labaran ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a taron tunawa da ranar hawan jini ta duniya, wanda aka gudanar a Kano.

 

 

A taron tunawa da ranar, ma’aikatar ta shirya wani tattaki da taron manema labarai da nufin wayar da kan jama’a game da cutar hawan jini da inganta rigakafinta, ganowa da sarrafa shi.

 

 

An fara tattakin ne a ma’aikatar lafiya ta hanyar gidan waya da karfe 8:30 na safe kuma aka kammala a cibiyar bayar da agajin gaggawa (EOC) da ke cikin asibitin Nassarawa, inda aka gudanar da taron manema labarai.

 

 

 

Dokta Abubakar Labaran ya ce taron wani bangare ne na kokarin da duniya ke yi na yaki da cutar hawan jini, babban kalubalen da ya shafi lafiyar al’umma da ya shafi manya biliyan 1.28 a duniya.

 

Ya kara da cewa gwamnatin jihar Kano ta ba da fifiko sosai wajen magance kalubalen da cutar hawan jini ke karuwa a tsakanin mutane, yana mai jaddada cewa gwamnati ta kafa cibiyoyin kula da masu fama da hauhawar jini a fadin jihar.

 

 

Cibiyar Kula da Cigaban Najeriya ta GAMMUN kuma tana aiki don samar da mafita mai ɗorewa ga masu fama da hauhawar jini ta hanyar shirye-shiryenta cikin watanni uku tare da manyan jami’an gwamnati.

 

Kwamishinan ya kara da cewa ta hanyar halartar bikin ranar hawan jini ta duniya, daidaikun mutane na iya daukar matakin da ya dace wajen kiyaye lafiyar zuciya da rage hadarin kamuwa da cutar hawan jini.

 

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka
  • Za’a Gudanar Da Tattaunawa Zagaye Na 5 Tsakanin Amurka Da Iran A Ranar 23-Afrilu A Roma
  • Xi Ya Jaddada Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaba Mai Inganci A Kasar Yayin Ziyararsa A Henan 
  • Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya
  • Shugaban Kasar Colombia: Ayyukan Kasar Sin Sun Nuna Wani Sabon Salo Na Ci Gaban Zamantakewar Al’ummar Bil’adama
  • Xi Jinping Ya Ziyarci Birnin Luoyang Na Lardin Henan
  • Hadin Gwiwa Bisa Daidaito Da Girmama Juna Tsakanin Sin Da Amurka Zai Samar Da Moriyar Juna
  • Sharhin Bayan Labarai: Dandalin Tattaunawa Na Tehran
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Fatan Tattaunawar Kasarsa Da Amurka Ta Cimma Yarjejeniya Ta Gaskiya
  • Kano Za Ta Yaki Cutar Hawan Jini Tare Da Hadin Gwiwar Kungiyar Global Effort