Leadership News Hausa:
2025-06-30@22:21:16 GMT

Yaukaka Zumunci Da Makwabta A Aikace Tsakanin Sin Da Malaysiya

Published: 16th, April 2025 GMT

Yaukaka Zumunci Da Makwabta A Aikace Tsakanin Sin Da Malaysiya

Kasar Sin ta kuma nuna aniyarta ta lale marhabin ga shigar da karin kayan amfanin gona masu inganci na Malaysiya zuwa katafariyar kasuwarta inda ta kuma nemi kasar ta Malaysiya ta kara bai wa kamfanoninta kwarin gwiwar zuba jari a kasar.

 

Kasar Malaysiya ta san irin alheran da kamfanonin Sin suke ci gaba da kawo mata wajen raya tattalin arziki da ci gaban masana’antunta.

Wannan ya sa Sultan Ibrahim ya bayyana cewa, Malaysiya tana dora fifiko sosai a kan zumuncinta da kasar Sin, kuma za su ci gaba da yin aiki tare domin samun nasara ga kowane bangare, tare da kara matsa kaimi ga gina al’umma mai makoma ta bai-daya a karkashin ingantattun manyan tsare-tsare kuma a duk wani sauyi da za a iya samu a duniya.

 

Tabbas, Malaysiya tana shaida irin ci gaban da kamfanonin kasar Sin suke kawo mata. Babban jami’in kasuwanci na tashar teku ta Kuantan, Mazlim Husin, ya bayyana yadda yankin masana’antu na hadin gwiwar Sin da Malaysiya (MCKIP) ya bude sabon babi ga bunkasa ci gaban Kuantan tun bayan kaddamar da shi a shekarar 2013. Kafa kamfanin mulmula karafa na Alliance Steel ya kara wa sauran kamfanoni kwarin gwiwar bude rassansu a yankin masana’antun wanda ya habaka samar da ayyukan yi da walwalar al’ummar wurin.

 

Kasar Sin ta kasance kasar da ta fi kowace kasa zuba jari a Malaysiya, inda ko a bara ta zuba kimanin dala biliyan 6.4 a kasar wanda ya kai kaso 16 na kudin shigar da Malaysiya ke samu daga zuba jarin kasashen waje kuma ana sa ran ya samar da sabbin guraben ayyukan yi 20,000.

 

Kazalika, wani jami’in ofishin jakadancin Malaysiya mai kula da zuba jari dake Guangzhou, Safwan Nizar Johari ya tabbatar da cewa akwai karin kamfanonin Sin dake zuba jari a kasar musamman a bangaren motocin sabbin makamashi, wanda hakan na nuna zumunci mai kyau tsakanin Sin da makwabtanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Malaysiya ta a Malaysiya

এছাড়াও পড়ুন:

Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara

Gwamnan Jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya ce zai iya yin komai muddin hakan zai kawo zaman lafiya da ci gaba a jiharsa.

Fubara, ya faɗi haka ne a garin Fatakwal a ranar Asabar, yayin da yake magana da magoya bayansa.

An samu amincewar yi wa Dantata jana’iza a Madina Van Nistelrooy ya ajiye aikin horas da Leicester City

Ya tabbatar musu cewa ya sasanta da Tsohon Gwamnan jihar, wanda a yanzu Ministan Abuja ne, Nyesom Wike.

Ya ce ya san wasu daga cikin magoya bayansa ba za su ji daɗin sasancin da aka yi ba, amma ya roƙe su da su yi haƙuri.

Ya ce: “Wani lokaci sai an ɗauki matakai masu wahala domin a samu gyara.”

Ya ƙara da cewa: “Kowa ya san mun yi iya ƙoƙarinmu. Amma yanzu abin da muke buƙata shi ne zaman lafiya.”

Fubara ya ce ba wanda zai iya musanta irin taimakon da Wike ya masa.

“E, mun samu saɓani a wasu abubuwa, amma ba za a iya cewa Wike bai taka rawar gani ba.

“Duk wanda ke sona da gaskiya, ya daina magana, lokaci ne na zaman lafiya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe
  • Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
  • Babu wanda zai manta da gudunmawar da Wike ya ba ni — Fubara
  • Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
  • An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
  • Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
  • An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
  • Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku
  • Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD