Leadership News Hausa:
2025-08-15@09:10:17 GMT

Yaukaka Zumunci Da Makwabta A Aikace Tsakanin Sin Da Malaysiya

Published: 16th, April 2025 GMT

Yaukaka Zumunci Da Makwabta A Aikace Tsakanin Sin Da Malaysiya

Kasar Sin ta kuma nuna aniyarta ta lale marhabin ga shigar da karin kayan amfanin gona masu inganci na Malaysiya zuwa katafariyar kasuwarta inda ta kuma nemi kasar ta Malaysiya ta kara bai wa kamfanoninta kwarin gwiwar zuba jari a kasar.

 

Kasar Malaysiya ta san irin alheran da kamfanonin Sin suke ci gaba da kawo mata wajen raya tattalin arziki da ci gaban masana’antunta.

Wannan ya sa Sultan Ibrahim ya bayyana cewa, Malaysiya tana dora fifiko sosai a kan zumuncinta da kasar Sin, kuma za su ci gaba da yin aiki tare domin samun nasara ga kowane bangare, tare da kara matsa kaimi ga gina al’umma mai makoma ta bai-daya a karkashin ingantattun manyan tsare-tsare kuma a duk wani sauyi da za a iya samu a duniya.

 

Tabbas, Malaysiya tana shaida irin ci gaban da kamfanonin kasar Sin suke kawo mata. Babban jami’in kasuwanci na tashar teku ta Kuantan, Mazlim Husin, ya bayyana yadda yankin masana’antu na hadin gwiwar Sin da Malaysiya (MCKIP) ya bude sabon babi ga bunkasa ci gaban Kuantan tun bayan kaddamar da shi a shekarar 2013. Kafa kamfanin mulmula karafa na Alliance Steel ya kara wa sauran kamfanoni kwarin gwiwar bude rassansu a yankin masana’antun wanda ya habaka samar da ayyukan yi da walwalar al’ummar wurin.

 

Kasar Sin ta kasance kasar da ta fi kowace kasa zuba jari a Malaysiya, inda ko a bara ta zuba kimanin dala biliyan 6.4 a kasar wanda ya kai kaso 16 na kudin shigar da Malaysiya ke samu daga zuba jarin kasashen waje kuma ana sa ran ya samar da sabbin guraben ayyukan yi 20,000.

 

Kazalika, wani jami’in ofishin jakadancin Malaysiya mai kula da zuba jari dake Guangzhou, Safwan Nizar Johari ya tabbatar da cewa akwai karin kamfanonin Sin dake zuba jari a kasar musamman a bangaren motocin sabbin makamashi, wanda hakan na nuna zumunci mai kyau tsakanin Sin da makwabtanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Malaysiya ta a Malaysiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin

Gwamnatin Iraki ta bayyana cewa: Yarjejeniyar da Iran ta kulla da Iraki zata yi gagarumar amfani a fagen tsaron yankin

Ofishin jakadancin Iraki a Amurka ya tabbatar da cewa: Iraki kasa ce mai cin gashin kanta kuma tana da hakkin kulla yarjejeniyoyin da kuma yarjejeniyar fahimtar juna. An yi nuni da cewa, yarjejeniyar tsaro da aka rattabawa hannu a baya-bayan nan tsakanin Iran da Iraki ta zo ne a cikin tsarin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu don tabbatar da tsaro da kuma kula da kan iyakokin kasashen biyu.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa: Ofishin jakadancin ya bayyana a cikin wata sanarwa da kamfanin dillancin labaran kasar Iraki INA ya watsa cewa: “A matsayin martani ga kalaman da kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta yi a yayin taronta na ‘yan jarida na baya-bayan nan, Iraki kasa ce mai cikakken ‘yancin kai, kuma tana da hakkin kulla yarjejeniyoyin da kuma bayanan fahimtar juna bisa tanade-tanaden kundin tsarin mulkinta da dokokin kasa, kuma ta hanyar da ta dace da manyan muradunta.”

Ta kara da cewa, “Iraki na jin dadin huldar sada zumunci da hadin gwiwa da kasashe da dama a duniya, ciki har da kasashe makwabta, Amurka, da sauran kasashe abokantaka, kuma tana da sha’awar gina wannan dangantakar bisa tushen mutunta juna da moriyar juna.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Yemen Sun Kai Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’Ila Har Sau Shida  August 13, 2025 Wakilan Hamas sun isa Alkahira don shawarwarin tsagaita wuta a Gaza August 13, 2025 Iran: Amurka Da Isra’ila Ne Da Kansu Suka Bukaci Dakatar Da Bude Wuta August 13, 2025 Habasha: Madatsar ruwanmu amfanin dukkanin kasashen yankin ne August 13, 2025 Bankin Duniya Zai Kashe $300m Don Inganta Rayuwar ’Yan Gudun Hijira A Arewacin Nijeriya August 13, 2025 Nijeriya Da Isra’ila Na Kara Karfafa Alaka A Tsakaninsu August 13, 2025 Kasashe 27 Sun Bukaci Isara’ila Ta Kawo Karshen Hana Shigar Da Abinci A Gaza August 12, 2025 Iran: Duk Wani Sabon Hari, Zai Fuskanci Mummunan Martanin Soji August 12, 2025 Larijani: Iraki Ba Ta Karbar Umarni Daga Iran August 12, 2025 Iran: Ma’aikatar Harkokin Waje Ce Ke Kula Da Lamarin Makamashin Nukliyar Kasar August 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INEC
  • Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin
  • Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 128
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 124
  • Ranar Matasa: Ciyaman ya jinjina wa gwamnatin Gombe kan ɗaukar matasa aiki
  • Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin
  • DAGA LARABA: Yadda sinadaran dandanon abinci ke yin illa ga lafiya
  • Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
  • Ministan Harkokin Wajen Iraki Ya Bukaci Zaman Tattaunawa Tsakanin Kungiyar Larabawan Yankin Tekun Gulf Da Iraki Da Kuma Iran