Shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammad Bakir Qolibof ya bayyana cewa kungiyar BRICS wata dama ce ta kaucewa danniya da babakeren da Amurka take kudaden sauran kasashen duniya.

Qolibof yana bayyana haka ne a lokacin ganawarsa da shugaban majalisar dokokin kasar Brazil Dowi Alku-Lomubre a gefen taron shuwagabannin majalisun dokokin kungiyar BRICS wanda ke gudana a halin yanzu a birnin Brazia na kasar Brazil.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shugaban majalisar dokokin Iran yana fadar cewa kasashen Iran da Brazil suna da fahinta iri guda dangane da yenci da kuma zama yentacciyar kasa. Don haka tare da wannan ana iya gina dangantaka ta bunkasar tattalin arziki tsakanin kasashen biyu tare da wannan fahintar.

Qolibof ya kara da cewa abu mafi muhimmanci na tattalin arzikin wanda kasashen biyu zasu fara karfafawa sun hada da ayyukan Noma musayar kayakin kasuwanci, na shigowa da fitarwa da kuma bangaren ilmi.

Ya kuma bayyana cewa a ganawarsa da ministan harkokin noma ya bayyana cewa abu na farko wanda kasashen biyu zasu yi shi tabbatar da kwamitin tattalin arzikin kasashen biyu ya fara aiki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya ce taron koli na Sin da kungiyar Tarayyar Turai ta EU karo na 25 dake tafe, zai taimaka wajen bunkasa tattaunawa bisa matsayin koli, da zurfafa shawarwari, da hadin gwiwa tsakanin sassan biyu, lamarin da zai biya bukatu da moriyarsu, da ma na sauran sassan duniya baki daya.

Guo Jiakun, ya jaddada muhimmancin taron, kasancewar ya zo a gabar da harkokin cudanyar kasa da kasa ke fuskantar yanayi na tangal-tangal, da ma karuwar daukar matakan kashin kai daga bangare guda, da kariyar cinikayya.

Ya ce, hadin gwiwar sassan biyu, ya haifar da manyan nasarori a baya, wanda hakan ya bunkasa ci gaba da daukakarsu, tare da samar da tarin alfanu ga jama’arsu da yawanta ya kai biliyan biyu, kana ya samar da babbar gudummawa ga raya zaman lafiya, da ci gaban duniya baki daya. Kazalika, hadin gwiwar sassan biyu ya zamo misali na hadin gwiwar cimma moriyar juna, a sabon zamani na dunkulewar tattalin arzikin duniya.

Daga nan sai ya bayyana aniyar kasar Sin ta yin aiki tare da EU, wajen cimma nasarar taron, matakin da zai aike da kyakkyawan sako ga duniya, game da aniyarsu ta hada karfi da karfe, wajen kafa hadin gwiwa mai karfin gaske, da daga martabar cudanyar mabambantan sassa, da bude kofa da aiwatar da hadin gwiwa. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin
  • Tursasawa Kasashen Afirka Karbar Bakin Haure Daga Amerika Kuskure Ne
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Sheikh Qasem: Nuna Halin Ko In-Kula Na Duniya Ne Ya Jawo Kisan Kiyashi A Gaza
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi
  • Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco