An haifi Peter Rufa’i a ranar 24 ga watan Agusta, 1963, a Oshodi, Legas, a wani gidan sarautar gargajiya, Mahaifinsa shi ne sarkin kabilar Idimu a Jihar Legas, duk da hasashen da ake yi na cewa zai yi gadon sarautar gidansu, Rufa’i ya yi watsi da sarautar don ci gaba da fuskantar abin da yake sha’awa wato kwallon kafa.

2. Ya yi Wasa A Manyan Kungiyoyin Kwallon Kafa A Kasashen Turai

Rufa’i ya fara sana’ar kwallon kafa a kungiyoyin gida Nijeriya kamar Storeery Stores da Femo Scorpions kafin ya tsallaka zuwa kasar waje, ya taka leda a kungiyoyi a kasar Benin (Dragons de l’Ouémé), Belgium (Lokeren, Beberen), Netherlands (Go Ahead Eagles), Portugal (Farense, Gil Bicente), da Spain (Hércules, Deportibo La Coruña), inda ya samu gogewa a bangaren da yake na mai tsaron raga.

3. Ya Taimakawa SC Farense Wajen Samun Damar Buga Kofin Turai (UEFA)

A lokacin kakar shekarar 1994–95, Rufa’i ya taka rawar gani wajen taimaka wa kulob din SC Farense na Portugal samun nasarar shiga gasar cin kofin UEFA na farko, ya ci gaba da zama a kungiyar inda aka zura masa kwallaye 38 kacal a wasanni 34 da ya buga a wannan kakar wasan.

4. Shine Mai tsaron Ragar Nijeriya Na Farko A Gasar Kofin Duniya

Rufa’i ya buga wa Nijeriya wasanni 65 na kasa da kasa, kuma shi ne mai tsaron raga na farko da Nijeriya ta zaba a gasar cin kofin duniya na FIFA a shekarun 1994 da 1998, ya kuma taka muhimmiyar rawa a gasar cin kofin nahiyar Afirka da Nijeriya ta yi a kasar Tunisia a shekarar 1994.

5. Ya Taba Ci Wa Nijeriya Kwallo

Yayin da ba kasafai ake samun mai tsaron raga ya ci kwallo a wasan kwallon kafa ba, Rufa’i ya zura wa Nijeriya kwallo a bugun fenareti a wasan da suka doke Habasha (Ethiopia) da ci 6-0 a wasannin neman gurbin shiga gasar AFCON a shekarar 1993, ita ce kadai kwallon da ya taba ci wa Nijeriya, kuma ta kasance daya daga cikin lokutan da ba zai taba mantawa da shi ba a rayuwarsa.

6. Ana Yi Masa Lakabi Da “Dodo Mayana”

Masoya nayi wa Rufa’i lakabi da “Dodo Mayana” saboda zafin nama da yadda yake tare kwallaye cikin kwarewa, lakabin ya zama tamkar wani kamanceceniya da yake yi da Dodo na asali duba da yadda yake yin abin da ba ayi tsammanin cewa zai iya yi ba.

7. Ya Yi Makarantar Aikin Horarwa Domin Samun Lasisin Horarwa

Bayan ya yi ritaya daga buga kwallon kafa, Rufa’i ya dawo aji a shekarar 2023, inda ya shiga Cibiyar kula da wasanni ta kasa da ke Legas don samun takardar cancantar zama koci, yana daga cikin babban kokarin da ya yi wajen ganin ya ci gaba da taimaka wa matasa masu tasowa wajen kwarewa da jagoranci a harkar kwallon kafa.

8. Ya Kafa Makarantar Kwallon Kafa ta Staruf

Mai himma wajen bunkasa matasa, Rufa’i ya kafa makarantar horar da kwallon kafa ta Staruf a Legas, har ila yau, ya kasance mai bayar da shawara akan a saka wasanni cikin jadawalin koyarwa a Nijeriya, ya kuma bukaci iyaye a Nijeriya da su yi kokarin cikar burin ‘ya’yansu na zama cikakkun yan kwallo tare da karatun Boko a lokaci guda.

9. Yana Da Matukar Jajircewa Akan Abin Da Ya Saka A Gaba

Rufa’i ya bayyana cewar tsawon shekaru 20 fa ya shafe a matsayin dan kwallon kafa bai rasa nasaba da yadda yake da jajircewa a duk abin da ya saka a gaba, inda yake cewa ina bayar da himma fiye da kashi 100 a koda yaushe, wadannan dabi’un, in ji shi, sun taimaka masa ya yi nasara a kasashe da dama da kuma fuskantar matsin lamba.

10. Yaba Karbar Laifinsa Idan Akayi Rashin Nasara

Duk da rawar da ya taka a fagen kwallon kafa a tsawon lokaci, rashin nasarar da Nijeriya tayi a hannun Denmark da ci 4-1 a gasar cin kofin duniya na shekarar 1998 a zagaye na 16 na daya daga cikin mafi munin wasannin da Rufa’i ya buga, ya bayyana shi a matsayin wasan da ya fi zafi a

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya a gasar cin kofin kwallon kafa wa Nijeriya da Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Tsohon Gwamnan Jihar Ribas ya yi gargaɗin cewa dogaro da soja kaɗai, ba tare da inganta rayuwar jama’a ba, zai ƙara haifar da rikice-rikice.

Ya ƙara da cewa ingantacce  tsaro na ƙasa yana farawa ne idan gwamnati ta ƙirƙiro damarmakin samun aiki da kuma mayar da amincin jama’a ga gwamnati.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa October 14, 2025 Manyan Labarai Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan October 14, 2025 Manyan Labarai Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026 October 13, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Trump bai cancanci mai samar da zaman lafiya ba yayin da yake haifar da yake-yake
  • Trump ya ce zai yi shawara game da batun kafa kasar Falasdinu
  • Ya kamata ‘yan fim su rika taimaka wa kananan cikinsu-Rukayya Abdullahi
  • Gwamnan Enugu Peter Mbah da kwamishinoninsa sun koma APC
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan
  • Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or?
  • Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Gwamna Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna