Mataimakin firaministan Sin Ding Xuexiang, ya yi kira a karfafa hadin gwiwa a bangaren tattalin arziki na zamanni ko kuma tattalin arziki na dijital.

Ding Xuexiang ya bayyana haka ne jiya Juma’a, yayin da ya halarci bikin bude taron kungiyar kasashen hadin kai ta Shanghai (SCO) kan tattalin arzikin dijital, a birnin Tianjin dake arewacin kasar Sin.

Cikin jawabinsa na bude taron, Ding Xuexiang wanda kuma mamba ne na kwamitin dindindin na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, bisa la’akari da damarmaki da kalubale da na’urori da fasahohin zamani suka zo da su, ya kamata a yi kokarin gaggauta aiwatar da muhimmiyar matsayar da shugabannin kasashen SCO suka cimma da kuma yarjejeniyar tafiyar da harkokin fasahohin zamani ta duniya.

Mataimakin firaministan ya kuma bayar da shawarar inganta hadin gwiwa a bangaren tattalin arziki na dijital da karfafa manufofin tuntubar juna da tsara burinkan ci gaba na kasashen ta yadda za su dace da juna da yin cikakken amfani da dandamalin hadin gwiwa kamar na taron na SCO kan tattalin arzikin dijital, domin kara wa kokarin raya bangaren kuzari. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 24 a Arewa maso Gabashin Nijeriya

Dakarun rundunar Operation Haɗin Kai sun yi nasarar kashe mayaƙan Boko Haram da ISWAP 24 a wasu sabbin hare-hare da suka ƙaddamar a maɓoyar ’yan ta’addan a yankunan daban-daban a Arewa maso Gabashin Nijeriya.

Kwamandan haɗakar rundunar Operation Haɗin Kai a Arewa Maso Gabas, Janar Abdulsalam Abubakar ya ce an kai samamen ne bayan tattara bayanan sirri.

A cewarsa, an kuma kashe mutum biyar da suke samar wa ’yan ta’addan kayayyakin amfani, a wani kwanton ɓauna da aka yi musu da daddare.

An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu

An gudanar da waɗannan ayyuka ne a tsakanin ranakun 4 zuwa 9 ga watan Yuli a Dajin Sambisa, da Dandalin Timbuktu da kuma Tsaunukan Mandara da ma wasu wuraren daban.

A yayin samamen, rundunar ta ce an yi nasarar ƙwato muggan makamai da dama da babura da kekuna da kayan abinci da kuma kaki da takalman sojoji.

Manjo Janar Abdulsalam ya ce rundunar hadin gwiwa ta bangaren sojin sama, da Civilian Joint Task Force, da na sojojin Nijeriya ne suka gudanar da aikin.

Shi ma Kakakin rundunar ‘Operation Hadin Kai’ Kyaftin Reuben Kovangiya, ya bayar da cikakken bayanin ayyukan a cikin wata sanarwa.

A ci gaba da gudanar da jerin hare-hare na hadin gwiwa a fadin Arewa maso Gabas, sojojin Operation HADIN KAI (OPHK) tare da hadin gwiwar rundunonin sojin sama da hadin gwiwar Civilian Joint Task Force da mafarauta, sun yi nasarar gudanar da samame a kan ’yan ta’addar Boko Haram/ISWAP daga tsakanin 4 zuwa 9 ga Yulin 2025 inda suka kawar da ’yan ta’adda da dama.

A daya daga cikin samamen da aka kai a Platari a ranar 4 ga watan Yulin 2025, yayin da sojojin suka yi kwanton ɓauna, sun far wa ’yan ta’addar JAS/ISWAP da ke kan babura da ke tafiya daga dajin Sambisa zuwa Dandalin Timbuktu.

Nan take aka fatattaki ‘yan ta’addan ta hanyar buɗe musu wuta, lamarin da ya kai ga halaka ‘yan ta’adda 3.

Kazalika, bayan samun bayanan sirri kan zirga-zirgar ’yan tada kayar bayan a kewayen yankin Komala, sojoji sun sake yi wa ’yan ta’adda kwanton ɓauna, inda suka kashe wani mayakin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; An Mika Batun Hakin Gwiwa Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA Ga Kwamitin Kolin Tsaron Kasa
  • Iran Ta Yi Tir Da Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Dorawa Ma’aikaciyar MDD
  • Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki
  • Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 24 a Arewa maso Gabashin Nijeriya
  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu