Leadership News Hausa:
2025-07-12@12:04:03 GMT

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Published: 12th, July 2025 GMT

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Har ila yau, manufar ita ce; don rage yawan asarar da manoma ke tabkawa, bayan sun yi girbin farko da kuma jawo hankalin matasan kasar, domin su rungumi aikin na noma; musamman wanda za su yi, su samu riba.

Kaddamar da Taraktocin na zuwa ne, daidai da lokacin da kasar ke ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan abinci, wanda ya kai sama da kashi 30 cikin 100, duba da cewa; noman da ake yi a karkara na ci gaba yin karanci.

Idan har an rabar da wadannan Taraktoci yadda ya dace tare da horar da manoman da za su amfana, an kuma tabbatar da ana bai wa Taraktocin kulawar da ta kamata da sayar da su cikin rahusa, hakan zai taimaka wajen samun kyakkyawan sauyi a fannin noman kasar, musamman a bangaren samun riba.

Sai dai, har yanzu; tambayar da ake ci gaba da yi ita ce, shin ko wannan shiri zai samar da kyakkyawan sauyi a fannin na aikin noman kasar?

Hakikanin Fannin Aikin Noma Don Samun Riba A Nijeriya:

Fannin aikin noman kasar, na samar da ayyukan yi sama da kashi 70 cikin 100, inda kuma fannin ya kasance kimanin kashi 34 cikin 100 na aikin da ake yi a kasar.

Amma duk da haka, har yanzu fannin kashi 26 kacal yake bayarwa a matsayin gudunmawa, don bunkasa tattalin arzikin kasar, wanda akasari hakan na faruwa ne, sakamakon yadda ake yin noma da kayan aiki na gargajiya.

Nijeriya da ke Afirka ta Kudu da Hamada, aikin nomanta ya yi kasa sakamakon rashin yin aiki da kayan noma na zamani. Ta kuma kasance, tana da kasa da karamin ma’auni na hekta da ya kimanin 0.3, wanda hakan ya saba da shawarar da Hukumar Kula da Abinci da Ayyukan Noma ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO) ta bayar na bukatar samar da hekta 1.5 na yin noma.

Bugu da kari, an rawaito Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima ya bayyana cewa; Nijeriya mai yawan al’umma sama da miliyan 210, amma abin takaici, kasar na da Taraktocin noma masu aiki daga tsakanin 7,000 zuwa 12,000 ne kacal.

A cewarsa, hakan ya sanya a shekaru da dama da suka gabata, aka gaza samun bukatar da ake da ita ta samar da yawan abincin da ya kai mililiyan 2.4, domin bukatar ‘yan kasar.

Sai dai, ana ganin bisa wannan sabon yunkuri na gwamnatin ta hanyar hadaka da kamfanin kera kayan aikin noma da ke Belarus, wanda aka kaddamar da aikin tare da AfTrade DMCC, hakan ya sa an samar da ingantattun Taraktocin noma 2,000 tare da samar da kayan haro 190 da sauran makamantansu.

A karkashin aikin, ana sa ran za a noma hektar noma sama da 550,000, wadanda za su samar da tan miliyan 2 na hatsi tare da samar da ayyukan yi, wadanda ba na kai tsaye ba kimanin 16,000 da kuma na kai tsaye kimanin sama da 550,000.

Kaddamar da Taraktocin da sauran kayan aiki, hakan zai taimaka wajen habaka aikin noma don samun riba da kara bunkasa samar da wadataccen abinci da rage shigo da kayan abinci cikin Nijeriya, wanda yanzu haka, wadanda ake shigo da su a duk shekara, kudinsu ya kai sama da dala biliyan 2.5

Samar Da Wadataccen Abinci Da Matsalar Samun Hauhawar Farashin Kayan Abinci A Nijeriya:

Duk da samar da albarkar hektocin noma da Nijeriya ke da su, wadanda suka kai miliyan 70.8 kuma ake noma amfanin gona kamar irin su; Masara, Rogo, Shinkafa da saurasu, amma kasar na ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan abinci.

Fannin shi ne kusan kashin bayan bunkasa tattalin arzikin kasar, amma sama da ‘yan kasar miliyan 100 ne a yanzu ke fuskantar karancin abinci, kuma suna ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan na abinci da kuma rashin wadatattun kudaden sayen kayan abincin.

Wannan adadin, ya nuna yadda yanayin hauhawar farashin ya yi kamari, musamman a Arewa ta Tsakiyar kasar, wanda ya kai kashi 29.43 a Arewa ta Gabas, ya kai kashi 29.72.

Bugu da kari, kididdiga ta nuna cewa; ‘yan Nijeriya miliyan 18.6 ke ci gaba da jure wa yunwa, inda kuma mutane miliyan 43.7, suka dauki matakin rage cin abincin da suke ciyar da iyalansu.

‘Yan Nijeriya miliyan 133 ke ci gaba da fuskantar karancin ababen more rayuwa tare da ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan abinci, wanda a watan Mayun 2025 ya kai kashi 21.14 tare da kuma fuskantar matsananciyar yunwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan hauhawar farashin kayan abinci

এছাড়াও পড়ুন:

Direba ya tsere da buhun masara 463

Ana zargin wani direban tirela ya gudu da buhunan masara 463 da aka aike shi da su, bayan da ya bai wa ɗan rakiyarsa guba a cikin shayi a yankin Maraban Jos da ke Jihar Kaduna.

Wani ɗan kasuwa da ke safarar hatsi daga Jihar Kano zuwa kamfanoni a sassa daban-daban na Nijeriya, Injiniya Jamilu Haruna, ya shaida wa Aminiya cewa direban da ya ɗora wa masara buhu 463 domin kaiwa kamfanin Olam da ke Ilorin a Jihar Kwara, ya gudu da kayan.

“Kuɗin kayan sun kama Naira miliyan miliyan ashirin da ɗaya da dubu ɗari shida da tamanin da shida da ɗari huɗu.

“Wallahi jarin nawa ke nan ɗungurungum na dora a motar,” in ji ɗan kasuwar, wanda ya bayyana cewa direban ya ɗauko masa masarar ce a cikin tirela ƙirar Hoho mai taya 18 daga yankin Doguwa a Jihar Kano.

Ya ƙara da cewa direban ya sami nasarar guduwa da kayan ne bayan da ya ba wa mutumin da aka haɗa shi da shi a matsayin ɗan rakiya guba a shayi, sannan ya jefar da shi ya gudu da motar maƙare da kayan.

Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m a hanyar Jos Ɗalibi ya ƙone budurwarsa mai tsohon ciki har lahira

“Dukkanin buhunan 463 na masara da wobil ɗin kayan ya kwashe da su ya tsere. Wasu jami’an ’yan kamasho da suka saba sama mana motocin haya sun shiga cikin binciken. Haka nan ’yan sanda na ci gaba da gudanar da bincike don gano inda direban yake,” in ji ɗan kasuwar.

A zantawarsa da Aminiya, Injiniya Jamilu, ya ce tun bayan faruwar lamarin har yanzu ba a sami gano direban ba balantana kayan, lamarin da ya ce ya yi sanadiyyar raba shi da duk jarin da yake juyawa.

Yadda abin ya faru — Mai kaya

Ya ce, “Mukan yi safarar masara mu kai wa kamfanoni a Kano da ma maƙwabtan jihohi, wacce muke siye a kasuwannin yankin Doguwa da Tudun Wada a Kano da kuma Saminaka a Jihar Kaduna.

“A wasu lokutan idan kayan suka yi yawa a wasu sassan na Arewacin Nijeriya, mukan kai kaya har irin su jihohin Kwara da Oyo da ma Legas.

“Wannan karon na haɗa kaya buhu 463, sai na sa ’yan kamasho a Unguwar Bawa su kawo min mota. To su akwai hanyar da suke bi su tantance sahihancin direba kafin su haɗa mu da shi, don mu ba huruminmu ba ne.

“To a haka ne ’yan kamasho suka samo mana direba, muka yi cinikin kuɗin mota Naira miliyan ɗaya da dubu hamsin. Aka kawo min mota muka loda kaya a kan za a kai su Ilorin. Kuɗin kayan kuma sun kama Naira miliyan 21,640. Wallahi jarin nawa ke nan ɗungurungum na dora a motar,” in ji shi.

Ya ce sukan haɗa direban da aka ba su da amintaccen ɗan rakiya daga wajensu, “saboda gudun halin wasu direbobin na yi wa kayan da aka ɗora musu ɗauki ɗai-ɗai idan babu idon mai kaya ko wakilinsa.”

Injiniya Jamilu ya ce, “Direban da ɗan rakiyar sun tashi da kayan daga Doguwa suka kwana a Unguwar Bawa saboda dare ya yi, gari na wayewa suka shiga Marabar Jos a Kaduna, sai direban ya ce su tsaya su yi gyaran ƙafar motar saboda sun ɗan shiga ramuka.

“A nan ne ma direban ya kira ni ya ce akwai ragowar cikon kuɗinsa Naira 350,000, na tura masa N100,000 zai yi gyara, na tura masa kuma muka yi waya da ɗan rakiyata ya ce lafiya kalau,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “To tun wannan ranar ta 25 ga watan Yunin 2025 ban sake jin ɗuriyarsu ba. Na yi ta kiran yaron nawa da shi direban amma ba na samun su. Har gari ya waye ina kira ban samu ba, sai na ɗauka ko sun shiga wuraren da hanya babu kyau ne ko kuma babu sabis.

“Kawai sai ga ɗan sanda ƙashegari ya zo gidana ya ce akwai wani yarona da aka tsinta

a sume, ‘an tsince shi ya biyo kaya za su Ilorin, sai direba ya ba shi shayi, tun da ya sha kuma a nan ya faɗi ya sume, mu kuma washegari muka zo muka gan shi, shi ne muka ɗauke shi muka kai asibiti, inda bayan ya farfaɗo ya ce mana daga Doguwa yake, ya biyo kayanka ne’.

“Da suka yi wannan bayanin ne na tabbatar musu da cewa kayana ne. Shi ɗan sandan da ya kawo mana wannan mutumin ma shi ne ya je ya kamo mana wannan ɗan kamashon da tun

Direban ya yi layar zana

ɗan kasuwar ya ƙara da cewa tun daga nan ne ma suka gano duk lambobin direban ma tuni ya watsar da su ya canza wasu, kuma har yanzu duk hanyoyin da suka bi “mun kasa gano ainihin lambar wayarsa, ko kuma motar.”

Sai dai ya ce wannan ba shi ne karo na farko da ɗan kamashon yake samo masa motar ɗaukar kayan ba, domin a iya bana ya ba shi mota sama da guda 11.

Amma ya ce, “Shi ma ɗan kamashon wani ya hada shi da direban, kuma wanda ya haɗa sun ma shi ma bai san ainihin adireshin direban ba.” Sai dai ya ce yanzu haka ɗan kamashon da kuma wanda ya haɗa shi da direban suna tsare a hannun ’yan sanda yayin da ake ci gaba da faɗaɗa bincike.

Injiniya Jamilu ya ce, “Shi kansa yaron motar da aka ba gubar sannan aka jefar da shi ya sha bin kayan a baya kuma an kai su lafiya, wannan ne karo na farko da aka sami matsala.

‘Na rungumi ƙaddara’

“Na ɗauki wannan a matsayin jarrabawa, amma ina ci gaba da addu’ar idan da rabo Allah Ya bayyana kayan, idan kuma babu, Allah Ya mayar min da mafi alheri,” in ji ɗan kasuwar.

Ya ce yanzu haka ’yan sanda na ci gaba da bincike a ƙarƙashin ofishin Mataimakin Kwamishinan ’Yan Sanda na Shiyyar Tudun Wada da ke Jihar Kano.

Da wakilinmu ya tuntubi Kakakin Rundunar ’Yan Sanda ta jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce ba shi da masaniya a kan lamarin, amma ya ba shi lokaci zai bincika.

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton ya ce yana kan binciken bai kai ga samun cikakken bayani a kan lamarin ba.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Direba ya tsere da buhun masara 463
  • Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi
  • FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
  • Gwamnan Zamfara Ya Raba Buhunan Taki 59,205 Ga Manoman Jihar
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
  • NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta
  • Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
  • Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista