Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Gabanin Taron Jam’iyyar
Published: 24th, July 2025 GMT
Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC kuma Gwamnan Jihar Imo, Sanata Hope Uzodimma, ya bayyana cewa Gwamnonin APC sun gudanar da wata muhimmiyar ganawa da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a Fadar gwamnati da ke Abuja.
Da yake zantawa da manema labarai na Fadar Shugaban Ƙasa bayan kammala taron, Gwamna Uzodimma ya bayyana ganawar da cewa “tattaunawa ce mai muhimmanci da Shugaban Ƙasa domin ƙarfafa jam’iyyar da kuma inganta ikon ta na samar da nagartaccen shugabanci ga ‘yan Najeriya”.
Ya ƙara da cewa, a matsayin su na gwamnoni, sun haɗu da Shugaban Ƙasa domin daidaita matsayin al’amuran jam’iyya da kuma muhimman abubuwan da suka shafi shugabanci.
Da aka tambaye shi ko ana sa ran yanke wasu manyan shawarwari ko takaddama a yayin Taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar APC da za a gudanar a gobe Alhamis, gwamnan ya ce, “Ba za mu iya cewa komai yanzu ba har sai mun isa wurin taron gobe.”
Ana sa ran taron na gobe Alhamis 24 ga watan Yulin 2025 zai tattauna kan muhimman batutuwa da suka shafi jam’iyyar da kuma tsara hanyoyin ci gaba da haɗin kai da inganci a harkokin ta.
Bello Wakili
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamnoni Shugaban Ƙasa
এছাড়াও পড়ুন:
Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari
A wani roko da wata kungiya da aka fi sani da Sokoto Heritage Reloaded Initiative ta yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya cika alkawarin da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya dauka a lokacin wata ziyarar aiki da ya kai a jihar.
An yi wannan roko ne a yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a jihar Sokoto, inda shugaban kungiyar Farfesa Uthman Abdulqadir, ya jaddada muhimmancin girmama abubuwan da Shagari ya bari.
Ya tuna cewa shugaba Buhari ya yi wannan alkawari ne a ziyarar da ya kai Sokoto.
Farfesa Uthman ya bayyana irin rawar da Shehu Shagari yake takawa wajen ciyar da ilimi gaba a Najeriya, inda ya bayyana cewa ya taka rawa wajen aza harsashin kafa Budaddiyar Jami’ar Nijeriya.
Ya bayyana Shagari ba wai kawai shugaba ba, a’a a matsayin alama ce ta tawali’u, rikon amana da kishin kasa, mutumin da ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa kasarsa hidima.
Farfesa Uthman ya bayyana kwarin guiwar cewa shugaba Tinubu, wanda ya shahara da mutunta shuwagabannin kasa da jajircewar hadin kai, zai gane muhimmancin tunawa Shehu Shagari.
Ya yi imanin cewa wannan aikin zai bayyana a fili karara Tinubu a matsayin jagora mai girmama kimar tawali’u, hidima, da kishin kasa.
Farfesa Uthman ya jaddada cewa sanyawa wurare sunayen Dattijai ba karamin alfanu ne ga rayuwa jama’ar ba.
Ya bayyana shi a matsayin muhimmin kayan aiki don ilimi, zaburarwa, da kuma kiyaye dabi’un da suka dace da al’ummomin yanzu da na gaba.
NASIR MALAL