Dakarun Kassam Da Sarayal Kuds, Sun Kai Wa ‘Yan Mamaya Hare-hare A Gaza
Published: 13th, July 2025 GMT
Dakarun rundunar “Shahid Izzuddin al-kassam’ da kuma ” Sarayal Kuds” sun sanar da kai jerin hare-hare akan sansanonin ‘yan sahayoniya a yankuna mabanbanta na Gaza.
A bayanin da dakarun ” Kassam” su ka fitar sun bayyana hare-hare masu yawa da su ka kai wa ‘yan mamaya, da su ka hada da tarwatsa motocin buldoza biyu samfurin D9 a unguwar Zaituna a cikin birnin Gaza.
Haka nan kuma sun kai wani harin a ranar 6 ga watan Yuli wanda su ka rusa tankar yaki ta “Mirkava” ta hanyar amfani da wata nakiya mai tsananin fashewa.
Bugu da kari , Kassam ta ce a ranar 9 ga watan Yuli din ta kai wani harin akan sansanin da kwamandoji masu bayar da umarnin yaki suke a gabashin unguwar ‘al-tuffah’ a gabashin birnin Gaza,wanda ya yi wa abokan gaba asara mai yawa.
Haka nan kuma maharban na Kassam sun yi nasarar harbe wani sojan HKI a yankin Abasan al-kabirah, a gabashin birnin Khan-Yunus dake kudancin Gaza.
Su ma dakarun ” Sarayal-Kuds” na kungiyar Jiahdul-Islami sun sanar da jerin hare-hare akan sansanoni mabanbanta na ‘yan sahayoniya da su ka hada da rusa motocin yaki irin su tankar “Mirkava’ a unguwar ‘ al-Tuffah’ a cikin birnin Gaza. Haka nan kuma dakarun sun sanar da rusa wata motar ta soja a cikin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Kashe Jami’in Sojan HKI A Gaza
Rundunar sojan mamaya ta sanar da kashe daya daga cikin jami’an sojojinta dake karkashin rundunar “Golani” a yankin Khan-Yunus dake Gaza.
Da safiyar yau Juma’a ne dai sojojin mamayar HKI su ka snar da cewa wani daga cikin mayakansu mai mukamin Captain ya halaka a Gaza, kuma tuni sun bude bincike akan abinda ya faru.
Rahoton tashar talabijin din ” Cane” ta HKI ya ambaci cewa, sojan da aka kashe yana cikin wadanda su ka kai hari a garin Khan-Yunus a jiya Alhamis.
Sojojin mamaya sun kai hari ne a cikin wani gida a ci gaba da kashe ‘yan gwgawarmaya da suke yi, sai dai ginin gidan ya rufta da su, bayan da nakiyar da take cikinsa ta fashe.
Tun a jiya Alhamis ne dai kafafen watsa labarun na HKI su ka fara Magana akan cewa sojojin da suke Gaza, suna fuskantar yanaki mai tsanani, da hakan yake nufin cewa an halaka wani adadi nasu.
An ga jirgin sama mai saukar angulu yana shawagi a yankin da aka yi kazamin fada a tsakanin ‘yan gwgawarmaya da kuma sojojin mamaya.
A cikin kwanakin bayan nan dai ‘yan gwgawarmaya suna kara samun nasarar halaka sojojin HKI da suke yi wa al’ummar yankin kisan kiyashi da kuma jikkata wani adadi mai yawa nasu.