An kone babur din ‘barayin waya’ a Kano
Published: 23rd, July 2025 GMT
Wasu fusatattun matasa sun banka wa wani babur din Adaidaita Sahu da ake zargin na barayin waya ne wuta a unguwar Sharada da ke cikin birnin Kano da safiyar Laraba.
Barayin da ake zargi dai sun shiga wata makaranta mai zaman kanta ne da ke Sharada mai suna Al-Abbas College, inda suka ce sun zo nema wasu yaransu gurbin karatu ne amma suka sace wayar shugaban makarantar.
Da yake zantawa da Aminiya, daya daga cikin malaman makarantar, Malam Sunusi Hamisu, da ya shaida yadda lamarin ya faru, ya ce, “Matasa ne guda biyu da suka ce sun zo neman gurbin karatu na yara guda biyu a aji biyu da aji uku na Firamare saboda sun ce sun canza gari ne sun dawo Kano daga Kaduna.
Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta“To ni ne ma na raka su ofishin shugabar makaranta, sai ta ce a kai su ofishin mai makarantar, inda ya yi musu lissafin kudin rajista da na fom, sai suka ce ya dauko musu. To ya tashi zai dauko musu sai wayarsa ta fado, inda nan take suka dauke ta suka gudu.
“Fitarsu ke da wuya sai ya duba ya ga bai ga wayarsa ba, sai ya bi su da gudu ya karbi wayar, a lokacin har sun riga sun cire ta daga cikin gidanta sun cire layin sun kuma kashe ta.
“Da ya biyo su sai suka gudu suka shiga Adaidaita Sahun da suka zo da shi wanda ya tsaya a bakin titi yana jiran su. Nan take sai suka gudu a cikin babur din sai malamin ya fada wa mutane ga barayin waya, inda mutane suka yi kukan kura suka kama su.
“Da direban babur din ya ga an cim musu za a kama su, sai ya gudu ya bar babur din da barayin biyu a ciki, wadanda su kuma aka kama su,” in ji Malam Sunusi.
Ya ce bayan kama barayin ne aka mika wa ’yan sanda su, babur din kuma aka shigar da shi cikin makarantar.
To sai dai ya ce bayan an shigar da babur din ne sai matasan unguwa suka yi zuga suna barazanar balla kofar shiga makarantar idan ba a ba su babur sun kona ba, wanda ala tilas aka ba su suka fitar da shi suka banka masa wuta a bakin titi.
Shi ma wani mutum da abin ya faru a kan idanunsa mai suna Abdullahi Musa, ya ce an lakada wa barayin dukan tsiya kafin an damka su ga ’yan sanda sannan a kona babur din nasu.
“Mun riga mun yanke shawarar duk lokacin da muka kama babur din barayi sai mun kone shi, ta haka ne za su shiga taitayinsu,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sharada
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.
A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.
Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.
Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.
Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.
“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.
Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.
Gwamnan ya kuma sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.
Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.
Usman Muhammad Zaria