Aminiya:
2025-11-03@04:03:13 GMT

An kone babur din ‘barayin waya’ a Kano

Published: 23rd, July 2025 GMT

Wasu fusatattun matasa sun banka wa wani babur din Adaidaita Sahu da ake zargin na barayin waya ne wuta a unguwar Sharada da ke cikin birnin Kano da safiyar Laraba.

Barayin da ake zargi dai sun shiga wata makaranta mai zaman kanta ne da ke Sharada mai suna Al-Abbas College, inda suka ce sun zo nema wasu yaransu gurbin karatu ne amma suka sace wayar shugaban makarantar.

Da yake zantawa da Aminiya, daya daga cikin malaman makarantar, Malam Sunusi Hamisu, da ya shaida yadda lamarin ya faru, ya ce, “Matasa ne guda biyu da suka ce sun zo neman gurbin karatu na yara guda biyu a aji biyu da aji uku na Firamare saboda sun ce sun canza gari ne sun dawo Kano daga Kaduna.

Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

“To ni ne ma na raka su ofishin shugabar makaranta, sai ta ce a kai su ofishin mai makarantar, inda ya yi musu lissafin kudin rajista da na fom, sai suka ce ya dauko musu. To ya tashi zai dauko musu sai wayarsa ta fado, inda nan take suka dauke ta suka gudu.

“Fitarsu ke da wuya sai ya duba ya ga bai ga wayarsa ba, sai ya bi su da gudu ya karbi wayar, a lokacin har sun riga sun cire ta daga cikin gidanta sun cire layin sun kuma kashe ta.

“Da ya biyo su sai suka gudu suka shiga Adaidaita Sahun da suka zo da shi wanda ya tsaya a bakin titi yana jiran su. Nan take sai suka gudu a cikin babur din sai malamin ya fada wa mutane ga barayin waya, inda mutane suka yi kukan kura suka kama su.

“Da direban babur din ya ga an cim musu za a kama su, sai ya gudu ya bar babur din da barayin biyu a ciki, wadanda su kuma aka kama su,” in ji Malam Sunusi.

Ya ce bayan kama barayin ne aka mika wa ’yan sanda su, babur din kuma aka shigar da shi cikin makarantar.

To sai dai ya ce bayan an shigar da babur din ne sai matasan unguwa suka yi zuga suna barazanar balla kofar shiga makarantar idan ba a ba su babur sun kona ba, wanda ala tilas aka ba su suka fitar da shi suka banka masa wuta a bakin titi.

Shi ma wani mutum da abin ya faru a kan idanunsa mai suna Abdullahi Musa, ya ce an lakada wa barayin dukan tsiya kafin an damka su ga ’yan sanda sannan a kona babur din nasu.

“Mun riga mun yanke shawarar duk lokacin da muka kama babur din barayi sai mun kone shi, ta haka ne za su shiga taitayinsu,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sharada

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya

Daga Ali Muhammad Rabi’u 

 

Gwamnatin Jihar Kwara ta kafa kwamitoci biyu domin tantance bayanan wadanda suka yi  ritaya a matakin jiha da  kananan hukumomi.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinar Kudi ta jihar, Dakta Hauwa Nuru ta fitar, ta bayyana cewa kwamitocin za su tantance tare da tabbatar da sahihancin bayanan wadanda suka yi ritaya, domin a biya su bisa lokacin da suka bar aikin gwamnati.

A cewarta, kwamitin mutum takwas da aka kafa don kula da kudaden ritaya na matakin jiha zai kasance karkashin jagorancin Mai Duba Asusun Jiha, wato (Auditor General), yayin da wanda ke kula da matakin kananan hukumomi zai kasance karkashin Mai Duba Asusun Kananan Hukumomi.

Sanarwar ta bayyana cewa babban burin kwamitocin shi ne tabbatar da cewa an tattara bayanan masu ritaya bisa gaskiya da adalci, tare da  biyan su kai tsaye ta asusun ajiyar banki.

Ta kara da cewa, mambobin kwamitocin sun hada da wakilan tsofaffin manyan sakatarorin, kungiyar tsofaffin ma’aikata, Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), da kungiyar kwadago ta TUC, da sauransu.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure