Tashar talabijin din ‘almayadin’ ta ce, wata majiya mai karfi a jamhuriyar Nijar ta ce; An kusa kusa kawo karshen sabanin dake tsakanin gwamnatin jamhuriyar Nijar da kamfanonin kasar China da suke aiki a fagen hako da tace man fetur, bayan da bangarorin biyu su ka yi nisa a tattaunawar da suke yi.

Sauyin da aka sami shi ne amincewar kamfanin man fetur na kasar China ( CNPC) da sauya tsohon manajan dake tafiyar da ayyuka a Nijar, da wani sabo kamar yadda gwamnatin Yamai ta bukata.

Su ma kamfanonin WAPCO da SORAZ za su dauki sabbin matakai na samar da sauye-sauye a cikin harkokin tafiyar da su.

Ana sa ran cewa, sabbin matakan da kamfanoni na China da Nijar suke dauka zai bude sabon shafi a alakar kasashen biyu da za ta kare manufofin kowane bangare.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

An kaddamar da shirin koyar da Sinanci mai taken “Hello China”, na gidan rediyon Nijeriya (FRCN), a Abuja babban birnin kasar. Kusan mutane 100, ciki har da jakadan Sin a Nijeriya Yu Dunhai da darakta janar na FRCN Mohammed Bulama ne suka halarci bikin kaddamarwar da ya gudana a jiya Alhamis.

Cikin jawabin da ya gabatar, Yu Dunhai ya ce kaddamar da shirin na koyar da Sinanci da gidan rediyon ya yi, zai samar wa ‘yan Nijeriya wani sabon dandali na koyon harshen Sinanci da fahimtar kasar Sin, tare da samar da kuzari mai dorewa ga hadin gwiwar moriyar juna a fannonin cinikayya da tattalin arzikin tsakanin Sin da Nijeriya

Daga ranar 16 ga wata ne za a fara watsa shirin na “Hello China” a fadin kasar, a kowacce ranar Laraba daga karfe 5 zuwa 5:30 na yamma. Shirin ya kunshi koyar da harshen Sinanci da karin haske game da ilimin tattalin arziki da kimiyya da zaman takewa da al’adun kasar Sin. Ana sa ran shirin zai zama wata sabuwar kafa da ‘yan Nijeriya za su samu cikakkiyar fahimta ta ainihin kasar Sin daga bangarori daban daban. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran:  Goyon Bayan Shugaban Gwamnatin Jamus Ga ‘Yan Sahayoniya, Yin Tarayya Ne A Fada Da Iran
  • Associated Press: Harin Iran Akan Sansanin Amurka Dake Kasar Qatar Ya Lalata Wata Cibiyar Sadarwa
  • FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
  • Matatun Man Fetur Na Nijeriya Ba Za Su Ci Gaba Da Aiki Yadda Ya Kamata Ba – Dangote
  • Kamfanonin Jiragen Ruwa Sun Yanke Hulda Da Isra’ila Saboda Matsalar Hare-Haren Kasar Yemen
  •  HKI Tana Cigaba Da Yi Wa Mutanen Gaza Kisan Kiyashi
  • Kwamandan Sojin Iran Ya Jaddada Kare Kan Iyakokin Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Sojojin Yemen Sun Nutsar Da Jirgin Ruwan “Eternity” Dake Hanyar Zuwa HKI