Mataimakin shugaban kasar na farko ya jaddada cewa: Kalmar “mika kai” ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron Iran

Mataimakin shugaban kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya jaddada cewa: kalmar mika wuya ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron kasar.

Arif ya ce: Kamar yadda kuke gani kalmar “mika kai” ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yana mai jaddada cewa, su mutane ne masu wayewa, tare da ingantaccen tarihin al’adu wanda ya wuce dubban shekaru.

Ba su neman yaki, kuma ba su fara shi ba. Sun yi imani da zaman lafiya da kwanciyar hankali, kuma a shirye suke don tattaunawa, amma ba za su mika wuya a kowane hali ba.

A wata hira da ya yi da KHAMENEI.IR, Aref ya jaddada cewa: An sha ambaton hakan, sannan kuma Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa ba za mu fara yaki ba, amma idan aka tsokani Iran, to Iran zata mayar da martani, kuma haka yake har yanzu. Maƙiya ‘yan sahayoniyya ba za a taba amince da su ba. An dai tsagaita bude wuta a kasar Labanon, amma kamar yadda ake gani bayan tsagaita wuta an samun adadin shahidai masu yawa. Sadaukarwarsu ta kasance domin kare Iran ce.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jaddada cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Kamaru: Jam’iyyun adawa sun ayyana Bakary a matsayin wanda ya lashe zaɓe

Jam’iyyun adawa a ƙasar Jamhuriyar Kamaru sun ayyana Issa Bakary Tchiroma a matsayin wanda lashe zaɓen shugaban ƙasar da gagarumin rinjaye.

Gamayyar jam’iyyun adawa da ƙungiyoyin fararen hula na Union for Change ta ce sakamakon da suka tattara daga fadin ƙasar da ƙasashen waje ya nuna Bakary ya samu kashi 60 zuwa 80 cikin ɗari na ƙuri’u a rumfunan zaɓe da dama.

Sun buƙaci Shugaba Paul Biya, wanda ke neman wa’adin mulki na takwas a zaɓen da ya gaggauta miƙa saƙon taya murna ga Issa Bakary Tchiroma.

“Muna kira ga shugaban ƙasa mai barin gado da ya gaggauta taya sabon shugaban ƙasa murna,” in ji ƙungiyar,” in ji wata sanarwa da shugabannin ƙungiyar, Anicet Ekane da Djeukam Tchameni, suka fitar a birnin Douala.

Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph

“’Yan Kamaru sun yanke shawara. Sakamakon da muke karɓowa daga sassan ƙasar da ma ƙetare ya nuna a sarari cewa, ɗan takarar talakawa, Issa Tchiroma Bakary, ne ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 12 ga Oktoba 2025,” in ji sanarwar.

Ƙungiyar ta zargi jam’iyyar mai mulki ta CPDM da ƙoƙarin amfani da “tsohuwar hanyar maguɗi,” amma ta ce duk da haka Bakary ya yi mata “mummunar kaye mara misaltuwa,”

Union for Change 2025 ta kuma roƙi hukumomin gwamnati da jami’an tsaro da su mutunta zabin al’umma da zaman lafiya, tare da kira ga ’yan ƙasa da su ci gaba da kasancewa cikin shiri domin kare zaɓinsu.”

Bakary, wanda tsohon minista ne a gwamnatin shugaba Paul Biya, an zaɓe shi a watan Satumba a matsayin “ɗan takarar haɗin kai na jama’a.”

Ƙungiyar, wadda rahotanni ke cewa ta ƙunshi fiye da ƙungiyoyi 50 na siyasa da na fararen hula, ta ce manufarta ita ce haɗa ɓangarorin adawa domin yin aiki tare wajen sauyin siyasa da sake gina ƙasa.

“Ƙungiyar Talakawa ce, wadda take buɗe ƙoa ga kowa — ɗan ƙasa ko ƙungiya, ciki har da waɗanda ’yan takararsu aka hana shiga zaɓen shugaban ƙasa ba bisa ƙa’ida ba,” in ji sanarwar.

Ƙungiyar ta bayyana kanta a matsayin sabuwar ƙarfi na farfaɗo da dimokuraɗiyya, tana mai alƙawarin sake gina Kamaru a cikin lokacin canji na shekaru uku zuwa biyar.

A lokacin da ake rubuta wannan rahoto, Hukumar Ƙoli ta Ƙasar ba ta fitar da sakamakon hukuma ba, lamarin da ake ganin zai iya ƙara ɗaga zullumin siyasa a kwanaki masu zuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Najeriya ta casa Jamhuriyar Benin 4-0
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
  • Iran Ta Jadda Cewa A Shirye Take Ta Kare Kanta A Duk Wani Yaki Wanda Makiya Zasu Dora Mata
  • Ma’aikatar Harkokin wajen Kasar Iran Ta Yi Tir Da Jawabin Trump A Knesset Ta HKI
  • Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan
  • Kamaru: Jam’iyyun adawa sun ayyana Bakary a matsayin wanda ya lashe zaɓe
  • Kungiyar Hamas Ta Mika Yahudawa 7 Daga Cikin 20 Da ke Hannunta  Ga Kungiyar Red Cross
  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Iran Ta Gayyaci Mukaddashin Jakadan Kasar Oman Zuwa Ma’aikatar Harkokin Wajenta
  • Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja