Daruruwan mazauna kauyen Fegin Mahe da ke yankin Ruwan Bore a karamar hukumar Gusau ta Jihar Zamfara, sun gudanar da zanga-zanga a gaban Gidan Gwamnati da ke Gusau, inda suka bukaci gwamnatin jihar ta dauki matakin gaggawa kan kisan gilla da ‘yan bindiga ke yi a yankinsu.

Masu zanga-zangar sun rike takardu masu dauke da rubuce-rubuce kamar su: “Muna bukatar zaman lafiya a yankunanmu” da “Gwamnati ta cika alkawarin da ta dauka”.

A cewar mazauna kauyen, harin ya faru ne da safiyar ranar Laraba, lokacin da wasu ‘yan bindiga dauke da manyan makamai suka afka wa kauyen, inda suka rika harbin mai-kan-uwa-da-wabi.

Al’ummar yankin sun bayyana harin a matsayin daya daga cikin mafi muni da suka taba fuskanta a ‘yan shekarun nan, wanda ya bar su cikin tsoro da fargaba.

Masu zanga-zangar sun ce manufarsu ita ce jawo hankalin gwamnati kan tabarbarewar tsaro a yankin da kuma bukatar daukar matakin gaggawa don dakile kisan fararen hula da ake ta yi ba kakkautawa.

Sun kuma koka da cewa har yanzu akwai gawarwakin wasu daga cikin mutanen da aka kashe a dajin, amma babu wanda ke iya dauko su saboda tsoron sake fuskantar hari  daga hannun ‘yan bindigar.

Har zuwa lokacin da ake hada wannan rahoto, ba a samu wata sanarwa ko martani daga gwamnatin jihar ba dangane da harin ko kuma zanga-zangar da aka gudanar.

 

Daga Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara

Aƙalla masallata 40 ’yan bindiga suka sace a wani masallaci da ke Gidan Turbe a Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara da safiyar wannan Litinin.

Majiyoyi sun ce an yi awon gaba da masallatan ne zuwa dazukan Gohori da ke yankin Tsafe.

Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas

Wannan harin dai kai tsaye masu ruwa da tsaki na kallonsa a matsayin kawo ƙarshen yarjejeniyar sulhu tsakanin ’yan bindigar da mahukuntan jihohin Zamfara da Katsina.

A baya-bayan nan ne jihohin Katsina da Zamfara suka ƙulla yarjejeniyar sulhu tsakaninsu da ’yan bindigar da suka addabi al’ummar jihohin arewa maso yammacin Najeriyar.

Yarjejeniyar sulhu da aka cimma a dajin Wurma ta samu halartan manyan ’yan bindiga irinsu Alhaji Usman Kachalla Ruga da Muhindinge da Yahaya Sani ( Hayyu ) da kuma Shu’aibu.

A ɓangaren mahukunta, akwai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi da kuma shugaban ƙaramar hukuma Babangida Abdullahi Kurfi.

’Yan bindiga sun saki wasu mutane da suke garkuwa da su a lokacin yarjejeniyar sulhun, tare da barin al’umma zuwa gonakinsu ba tare da wata fargaba ko tsangwama.

To sai dai kuma, ƙasa da wata guda bayan cimma wannan yarjejeniya, rahotanni sun ce ’yan bindiga sun kutsawa wani ƙauye a Zamfara tare da awon gaba da masallata.

Shaidun gani da ido sun ce, maharan sun yi wa masallacin ƙawanya da misalin ƙarfe 5:30 na safe, daidai lokacin da jama’a ke sallar asuba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin