Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Published: 13th, July 2025 GMT
Ko za ka iya fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?
An haife ni a Unguwar Adakawa cikin birnin Kano, na yi makarantar firamare a Adakawa, daga nan kuma na tafi zuwa makarantar sakandire (Gwammaja One), bayan na sauke Alkur’ani, daga baya na tafi sai na wuce zuwa ‘School of Health Technology’ ta Kano.
Kamar wane irin kasuwanci kake yi?
Ina harkar takalma ‘yan Kofar Wambai, wadda ita ce sana’ar dana fara koya, sannan kuma ita ce sana’ar da dangina suke yi.
Me ya ja hankalinka har ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood?
Tun ina yaro na fara was an Dirama, daga makarantar firamare har zuwa sakandire, muna da ‘Drama club’ kafin zuwan kannywood.
Idan na fahimce ka, ba a shirin Dadin Kowa ka fara fitowa ba, ka fara ne daga wasan tun daga was an Dabe?
Tun kafin Dadin Kowa, an saba gani na a fina-finan Kannywood, na fara yin shuhura ne a fim din Mugun Iri, na Musa Mai Sana’a.
Daga wancen lokacin zuwa yanzu, ka yi kamar shekara nawa da fara wannan harka ta fim?
Fina-finan kannywood, na dauki kamar tsawon shekara goma sha biyar, amma na Dirama, na fara tun a shekarar 1998.
Yaya gwagwarmayar farawar ta kasance a wancan lokacin?
Dama kowa ya san dan ‘Drama Club’ ne ni, domin kuwa muna tare da su Tahir Fagge.
Yaya batun kalubale, musamman kai da taso a cikin gari, ka fuskanci tsangwama ko wani abu makancin haka daga iyaye, ‘yan’uwa sauran al’ummar unguwa?
Babu wani kalubale, kasancewar yaro ne mai biyayya da girmama na gaba, kuma iyaye suna kaunar ganin ci gaban duk abin da na dauko mai amfani da bai saba wa shari’a ba.
Ya farkon fara saka maka Kyamara ya kasance?
Ko kadan ban samu matsala wajen dora Kyamara ba, sakamakon na saba da ita, domin tun wajen shekarun 1984 ina cikin yara ‘yan rawar Bungalo, sannan kuma ina cikin wadanda ake nunawa a Talabijin.
Ko za ka iya bambanta wa masu karatu tsakanin wasan Dabe da na Kannywood?
Gaskiya bambancin shi ne, wasan ‘Drama club’, rukunin mutane ne kawai na masu ra’ayin shirya wasannin gargajiyya a fili ko dandali, wanda aka fi sani da wasan Dabe. Hanyar shiga kuma ita ce, kawai yawan zuwa wajen wasan da kuma yin abin da ake so ka yi.
A wasannin Dabe, ana tsara muku yadda za ku yi wasan ne kafin lokacin, ko kuwa yaya abin yake?
A wajen ake shirya wasannin, sannan kuma a yi bitar wasan, daga nan kawai sai kan Dandamali, wato ‘stage’, har ma wasu sukan ce ‘Stage Drama’.
Su waye abokan sana’arka wadanda ku ka yi wasan Dabe tare a wancen lokacin?
Abokan ‘stage drama’ na su ne; Tahir Fagge, Iyantama, Baba Labaran, akwai kuma irin su Aminu Boss da dai sauransu.
Yaya aka yi ka tsinci kanka cikin shirin Dadin Kowa?
To maganar Dadin Kowa, ‘audition’ aka yi na shiga, kuma ban samu nasara ba, na yi hakuri aka kuma sanya wani ‘audition’ din, bayan wani lokaci na kuma zuwa, a wannan karon sai na samu nasarar shiga.
A shirin Dadin Kowa, wane waje ka fi so, wane waje ne idan ka tuna yake ba ka dariya, sannan wane waje ne kuma ya fi bata maka rai?
A shirin Dadin Kowa wajen da ya fi ba ni dariya shi ne, lokacin da ina Hidimasta’, inda ‘yan kwamitin P.T.A suka taru za su cire ni daga mukamin, ni kuma na raba kansu na bai wa wasu shugabancin suka koma rigima a junansu. Sai kuma wajen da na kwashe shinkafar ‘yan makarantar na sayo gero, maimakon a rika dafa shinkafar aka koma dama Koko, yara suka rika sha suna barci a makarantar, nan ma ya ba ni dariya. Wajen da ya fi bata min rai kuma shi ne, lokacin da na sayar da gidan marayu na zuba kudin a caca aka cinye, wanda dalilin haka yasa na gudu daga garin Dadin Kowa.
Wane irin kalubale ka taba fuskanta, wanda ba za ka taba iya mantawa da shi ba, tun daga kan wasan Dabe, har kawo yanzu da ka ke cikin masana’antar kannywood?
Akwai kalubale da yawa, amma daya daga ciki shi ne; lokacin da na karbi aikin wani Darakta, aka sanya ranar aikin, amma na tashi da rasuwar kakana, bayan an yi masa wanka da ni, sai na tafi wannan aikin ba tare da na je jana’izarsa ba.
Wane irin nasarori ka samu game da fim?
Na samu nasarori masu yawa.
Ko za ka iya tuna yawan fina-finan da ka fito ciki?
Gaskiya akwai fina-finai da dama, kamar irin su; Ruwan Dare, Rariya, Garbati, Hannu da Hannu, Dangin Miji, Namijin Kishi, Sarah, ‘Yan Bodin da sauransu. Akalla za su kai kusan 80, wasu suna rubuce.
A finafinan da ka fito a ciki, wanne ka fi so; kuma me ya sa, sannan akwai wanda ka taba da-ka-sanin fitowa ciki?
Gaba-daya a fina-finan da na yi, na fi son Dadin Kowa, saboda shi ne ya fito da ni daga karamin jarumi zuwa babba.
Wace rawa ka fi yawan takawa a fina-finan da kake fitowa a ciki?
Na fi taka rawar mahaifi mai zafin gaske.
Da wane jarumi ko jaruma ka fi jin dadin yin aiki, kuma me ya sa?
Jarumar da na fi jin dadin aiki da ita ita ce, Zuwaira Abdulsalam, saboda ta san yadda za ta sanya ni na yi fushi ko kuma ta sauko da ni idan na yi fushin.
Ko akwai wata jaruma da ta taba yunkurin ganin ka aure ta a masana’antar?
Babu wata da muka taba ko soyayya, ballantana maganar aure.
Ko akwai jaruman da kake sa ran yin fim da su, wadanda ba ka taba yi da su a baya ba?
Ai babu wani jarumi da ya shahara kowaye da ban yi fina-finai da shi ba.
Wane ne babban abokinka a cikin masana’antar Kannywood?
Babban abokina a Kannywood shi ne; Hamisu Lamido Iyantama.
Bayan taka rawa da kake yi a matsayin jarumi ko akwai wata rawa da kake takawa a masana’antar?
Iya Jarumi ne n, ban taba shirya nawa fim din ba, kuma ba ni da niyya, sai dai nan gaba ta Allah ce.
Yaya kake hada aikinka na fim da kuma sana’arka ta takalmi?
Hada harkokina da na harkar fim ba matsala, domin kafin ranar aikin za a sanar da kai, saboda haka sai ka saita harkar ka da kuma ‘location’ din da za ka je.
Idan yaronka na sha’awar harkar fim, za ka ba shi dama ya yi?
Hahh..! ai ko waye cikin yarana yake da sha’awar yin fim, zan goyi bayansa har da gudunmawa.
Yaya mu’amularka sauran mutane, musamman wadanda zama ya hada ka da su?
Gaskiya wajen mutanen gari, babu wata matsala tsakanina da su, illa soyayya da son barka.
Mene ne burinka na gaba game da fim?
Burina na ci gaba, ganin masanaantar ta dawo da darajarta da hada-hadar sayar da aikin da masu ‘producing’ suka kashe kudi a kai.
Idan ka zama shugaba a masana’antar Kannywood, wane irin ci gaba za ka kawo wa masana’antar?
Da za a ce zan zama shugaba, zan yi kokari wajen kawo hadin kan manyan jarumai na masanaantar, sannan kuma zan bayar da shawara kan yadda za a yi hada-hadar kasuwar sayar da fina-finan, domin babbar matsalar harkar sayar da aikin, musamman kananan masu shirya fim din. Babban abin da ya kamata a gyara shi ne, kula da jarumai; domin har yanzu wasu masu biyan aikin ba su fahimci abubuwan sun canja ba.
Kenan kana nufin, akwai bukatar karin kudi ga su jaruman, kasancewar komai ya yi tsada a halin yanzu ko yaya kake nufi?
Kwarai kuwa, akwai bukatar kara kulawa da jarumai ta kowace hanya, musamman kasancewar mafi yawan jarumai ba masu karfi ba ne, kuma manyan jaruman da suka yi kudi su taimaki na baya.
Yaya kake kallon yadda fina-finai yanzu suka koma masu dogon zango, madadin yadda ake yi a baya na takaitaccen lokaci, shin hakan ci gaba ne ko kuwa ci baya ne a harkar?
Gaskiya fina-finan yanzu masu dogon zango ci gaba ne sosai, kuma da yawansu ina ciki.
Kana da ubangida a masana’antar Kannywood?
Gaskiya ba ni da ubangida kai tsaye, amma akwai wadanda suka taimake ni kwarai da gaske.
Wane kira kake da shi ga masoyanka, har ma da sauran masu kallon fina-finanka?
Kirana ga masoya na shi ne, duk lokacin da suka ga na yi wani abu wanda ba haka suke so ba, to su yi min uzuri; ita harkar fim ba ka umarni ake yi, ba kai ne kake yin abin da kake so ba, akwai mai bayar da umarni.
Ko kana da wadanda za ka gaisar?
Ina gaida Sadik Sani Sadik, Isa feroz Khan, Darakta Yaseen Auwal, Musa Mai Sana’a, Sarari classikue da dukkanin sauran abokan aiki.
Muna godiya da ba mu lokacinka da ka yi.
Ni ma na gode.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Barau Dadin Kowa
এছাড়াও পড়ুন:
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari
A daya bangaren kuma
Fita zuwa wani yanki daban da ba naka a halin yanzu, yana da nasa fa’idar. Domin kuwa, na ziyarci wasu jihohi uku kwanan nan; wadanda labarai a kansu babu dadin ji. Jihohin su ne, Delta, Inugu da kuma Zamfara, wadanda galibi labaransu marasa dadi ne ta fuskar siyasa, ta’addanci da sauran munanan laifuka. Daga labarun da ake samu yau da kullum, za ka yi tsammanin cewa; wadannan jihohi tuni sun tashi daga aiki, amma daga ziyarar da na kai musu; na ga abubuwan ban mamaki, tsoratarwa da kuma hadari duk da ke dauke cikin wannan labari.
Duk da cewa, kowace jiha akwai abubuwan da ta fi bai wa muhimmanci, su ma kamar sauran jihohin; suna fuskantar kalubale na yi wa al’umma aiki ta hanyar samar da damammaki, rage talauci da kuma tsantseni wajen sarrafa dukiyar al’umma.
Duk da cewa, har yanzu akwai sauran rina a kaba, amma abin da na gani a dan wannan lokaci da na ziyarci wadannan jihohi uku, tattakina zuwa Jihar Zamfara; shi ne mafi matukar tsoro a wajena
Zuwa Gusau
A karon farko da aka gayyace ni zuwa babban birnin jihar, Gusau, sai na yi watsi da tafiyar. Domin kuwa, a tafiya irin wannan akwai bukatar yin tunani da nazari mai zurfin gaske, musamman ganin yadda nake samun munanan labarai a kan Ado Aliero da sauran tawagarsa ta ‘yan ta’adda da ke yankin.
Har ila yau, sai aka sake turo min da wata gayyatar. Amma dai, a wannan karon akwai dan kwarin gwiwa, musamman ganin cikin tawagar da zan bi na tattaunawa ta farko da za a yi da Gwamna Dauda Lawal kai tsaye a kan wa’adin shekaru biyu da ya kwashe kan mulki. Tawagar ta kunshi; Gbenga Aruleba daga gidan talajin na AIT, Reuben Abati, ARISE TB da matarsa, Kiki, sai Ahmed Shekarau daga Media TRUST, Onuoha Ukeh daga SUN da kuma Babajide Otitoju, wanda Olajumoke Olatunji ya maye gurbinsa daga TBC.
ChatGPT da Gusau
Amma fa akwai matsala. Ta yaya za mu isa Gasau, duk da sanin abin da muka sani, na tambayi ‘ChatGPT’. Sai amsa min da cewa, kada ku tafi idan har tafiyar ba mai muhimmanci ba ce.
Ya ba da sanarwar tafiye-tafiye daga ofishin harkokin waje na burtaniya, Australia, Canada da kuma Amurka tare da gargadi game da tafiye-tafiye saboda tashin hankali, ta’addanci da kuma garkuwa da mutane, yana mai bayyana cewa; “Babbar matsaya daga hukumomin kula da tafiye-tafiye, ba ta ba da shawarar yin tattaki zuwa Jihar Zamfara, idan har ba akwai bukatar yin hakan ba.
“Titin Zariya zuwa Zamfara, musamman Funtua da ke Jihar Katsina, Tsafe, Maru-Dansadau, an bayyana su a matsayin wasu yankuna na mutuwa, wato wani filin wasa ne na Dogo Gide da Bello Turji, wanda tawagarsu ta ‘yan ta’adda suka kashe matafiya akalla 20, kamar yadda rahoton AP ya bayyana a watan Afrilun wannan shekara. Ina kan hanya, amma na kudiri niyyar tafiya.
Mutuwa da dawowa
Na yi ta mutuwa ina dawowa a cikin awa biyu da minti sha biyar, tsoro ya gama kama ni tare da alhinin cewa; idan na mutu a shekara 60, ba wai na mutu da kuruciya ba ne. Ban san cewa, matata ta lallaba ta sanya min wani abin kariya a cikin wata ‘yar karamar kwalba.
Gaba-daya ban lura ba, sai da na dawo daga tafiyar ina goge jakata, wannan ya isa ta bugi kirji da cewa; ta taimaka min da wani sirri na kariya. Na kasance a ankare cikin tsawon wannan tafiya ta kimanin kilomita 450 daga Abuja, cike da dimuwa.
Abin da ya ba ni mamaki, titin da ke tsakanin Zaiya da Katsina, mai layi biyu ne, sannan kuma yana da kyau sosai; titin bai tsuke ba sai da muka shiga Katsina, kana kuma ya sake bude bayan mun yi nisa ga duwatsu masu ban sha’awa da tsaunika da dukkanin bangarorin titin biyu. Amma titin Abuja zuwa Kaduna, abin kunya ne idan aka kwatanta shi da wannan, amma duk da haka; babban titin Abuja zuwa Kadunan ya lalace, kai ka ce shi ne kofar shiga Arewa Maso Yamma.
Fargaba da dimuwa…
Bayan Zariya, a wasu lokuta, mun wuce garuruwa masu yawan jama’a, amma mafi shahara a cikinsu shi ne garin Funtua, garin wasu daga cikin jiga-jigan ‘yan siyasa da suka hada da marigayi Malam Ismail Funtua da kuma fitaccen dan kasuwa, Umaru Mutallab.
Kowa ya yi tsit, kuma na kasa tambayar kaina cewa; ko mutanen da ke zaune a kauyukan da kananan garuwan da muke ratsawa, sun san abin da ake fada game da su kafafen yada labarai? Yayin da muka shiga Tsafe, garin daya daga cikin manyan ‘yan ta’addan da suka yi kaurin suna wajen garkuwa da mutane, wadanda suka samu nasarar share wajen zama a Jihar Katsina kafin ziyarar tamu, duk gashin da ke jikina sai da ya tashi.
Duk da cewa, mun samu rakiyar jami’an ‘yansanda ga kuma shingayen sojoji da dama a hanyar, yayin da muka isa Tsafe, kilomita 48 zuwa Gusau, ba ku ga irin tsoro da firgicin da ke cikin motarmu ba. shiru kake ji kowa ya yi dif.
Bayan Tsafe, na yi zaton tashin hankali ya kare a wannan tafiya. Sai kuma na ji na samu sauki tare kuma da shiga rudani da muka shiga Gusau. Saukin shi ne da muka isa lafiya, rudanin kuma saboda titi mai hannu biyu da ake dab da kammala, wanda ya hade da na Zamfara mai tattare da hadari da ban tsoro a tare da shi.
An samu canji
Ashe da rabon zan ga irin wadannan al’amuran a Enugu, inda rabo da zuwa tun
2006 (lokacin Chimaroke Nnamani yana gwamna). Ziyarar da na yi zuwa Zamfara na yi ta tun a farkon shekarun 1990, lokacin tana hade da Jihar Sakkwato
Jiha
Bayan wani Kantoman Mulkin Soji daya, da kuma wasu gwamnonin farar hula hudu, kafin Dauda, na biyar, Zamfara ta kasance wani abu kamar tallan shirin wasan kwaikwayo na Kannywood, inda ‘yan siyasa ke kwashe dukiyar kasa, ciki har da jama’arta, tare da nuna iko ko shakka babu Dauda zai iya nuna bambanci a wannan tsari. A cikin shekaru biyu, ya inganta asibitocin tuntuba da ke Gusau zuwa asibitin koyarwa mai dauke da wasu kayan aiki na zamani, ya kuma inganta harkar samar da ruwan sha, sannan ya kawar da koma bayan kudin WAEC da NECO na dalibai, lamarin da ya sa jihar ta kasance da ta samu kyakkyawan sakamako na tsawon shekaru. Haka kuma ya gina sabon filin jirgin sama wanda za a iya budewa kafin Satumba.
Gwamnati ta ce ta biya basussukan gratuti da kuma fansho ga ma’aikatan kananan hukumomi da na jiha tun daga shekarar 2011, da aka kiyasta kudin sun kai Naira biliyan 13.6, baya ga biyan bashin albashin watanni hudu da ya gada tare da kara mafi karancin albashi daga Naira 7,000 duk wata zuwa Naira 70,000.
“Komawar harkoki”
A lokacin da ake tattaunawar kai tsaye da Abati ya tambayi Dauda yadda ya sanya jihar a kan turba mai ban sha’awa, ciki har da ba ta wutar lantarki ta farko tun bayan da aka kirkiro ta shekaru 29 da suka gabata, gwamnan ya ce hakan ya faru ne ta hanyar toshe leken asiri ta hanyar amfani da fasaha, da kuma ba da fifiko wajen bunkasa albarkatun jama’a da kuma inganta karfinsu.
Ya ce an kuma yi amfani da fasaha don tattarawa da yin amfani da bayanan sirri don gina jiha mafi aminci, yana mai shan alwashin cewa ba za ai yi sulhu da ‘yan fashi da masu laifi ba.
Idan rayuwar dare ta daidaita a Gusau, babu shakka dukkan jama’ar da suka rasa matsugunai da wuraren sana’a za su dawo inda suke musamman gonaki a hankali. Wannan kuma wani hangen nesa ne da mutum zai iya duba jihar da aka ayyana kusan shekaru talatin ta hanyar cusa tsattsauran ra’ayi na addini, sata da kuma ‘yan fashi.
Ishiekwene Babban Editan LEADERSHIP kuma mai Rubuce-rubuce a Kafofin watsa labarai da harkokin Kudi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp