Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule Lamido
Published: 23rd, July 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya zargi Shugaba Bola Tinubu da amfani da hukumomin gwamnati wajen danne ’yan adawa.
Ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi da manema labarai a Kano.
Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa An kone babur din ‘barayin waya’ a KanoLamido, ya ce hukumomi irin su EFCC ana amfani da su ne wajen matsa wa ’yan adawa lamba.
Ya bayar da misalin tsohon Gwamnan Delta, Ifeanyi Okowa, wanda ke fuskantar tuhuma kan zargin aikata almundahana.
A cewarsa bayan Okowa ya koma jam’iyyar APC, an daina tuhumarsa.
Ya kafa misali da wata magana da Sanata Adams Oshiomhole ya taɓa yi.
Ya ce: “Da zarar ka shiga APC, an yafe maka zunubanka.” (Ko da yake Oshiomhole ya musanta yin wannan magana).
Lamido, ya gargaɗi gwamnati cewa amfani da ƙarfin iko wajen azabtar da ’yan adawa zai zama barazana ga dimokuraɗiyya.
Ya ce yanzu Najeriya na fama da rashin tsaro, rarrabuwar kawuna da rashin amana, wanda shi ne abin da ya fi dacewa gwamnati ta mayar da hankali a kai.
Ya kuma soki yunƙurin da ake yi na kafa jam’iyyar haɗaka kafin zaɓen 2027.
Lamido, ya ce duk wani yunƙuri na kafa sabuwar ƙungiya ya zama wajibi ya dogara da manufofi masu amfani kamar dimokuraɗiyya, zaman lafiya, tsaro da cibgaban ƙasa, ba kawai burin mulki ko ramuwar gayya ba.
Duk da matsalolin da PDP ke fuskanta, Lamido, ya ce har yanzu yana da kishin jam’iyyar.
Amma ya ƙara da cewa, matuƙar PDP ba za ta samar da abin da ake so, zai mara wa wasu muddin hakan zai amfani ƙasa.
Game da zargin cewa yana yi wa jam’iyyar adawa aiki, Lamido ya ce: “Ina ƙoƙari ne na dawo da jam’iyyar PDP kan turbar da ta dace.”
Ya kuma zargi wasu gwamnonin PDP da yin aiki da Tinubu a ɓoye ba tare da an hukunta su ba.
Ya ce PDP sai ta dawo kan tsarin gaskiya, adalci da dimokuraɗiyya idan tana so ta dawo da ƙarfinta.
“Ƙasar nan na cikin matsala ga yunwa, talauci, da rashin tsaro sun yawaita,” in ji shi.
Game da batun ƙirƙiro sabbin jihohi, Lamido, ya ce wannan ra’ayi yana da kyau amma ba yanzu ne lokacin da ya dace a bijiro da shi ba.
Ya ce ya fi dacewa a mayar da hankali kan warware matsaloli kamar rashin tsaro da yunwa.
Da aka tambaye shi game da ziyarar jagoran NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya kai wa Shugaba Tinubu, Lamido, ya ce bai da abin cewa.
“Kwankwaso da Tinubu na da ‘yancin su gana. Ku tambaye shi da kanku,” in ji shi.
A ƙarshe, Lamido, ya ce mafitar Najeriya na cikin dawo da amana, gaskiya, da bin doka a harkokin siyasa da gwamnati.
“Ina tare da PDP ɗari bisa ɗari, amma idan mafita ga Najeriya tana wajen PDP, zan bi ta domin Najeriya ta fi komai muhimmanci,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Adawa Kwankwaso Tsara yunwa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
A wani gagarumin mataki na karfafa yaki da rashin tsaro, gwamnatin jihar Zamfara ta gudanar da wani babban taron masu ruwa da tsaki a harkar tsaro a Gusau, da nufin karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomi da kuma kaddamar da sabbin dabarun yaki da ayyukan ta’addanci da masu aikata laifuka.
Taron wanda aka gudanar a Sakatariyar JB Yakubu wanda ofishin sakataren gwamnatin jihar (SSG) ya shirya, ya hada manyan hafsoshin tsaro, manyan jami’an gwamnati, da wakilan hukumomin tarayya domin duba halin tsaro da jihar ke ciki.
A cewar wata sanarwa da babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga SSG, Suleman Ahmad Tudu, ya yi, an kira taron ne domin zurfafa hadin kai a tsakanin masu ruwa da tsaki domin kara inganta ayyukan da ake gudanarwa a fadin jihar.
Sakataren gwamnatin jihar, Malam Abubakar Nakwada, wanda ya jagoranci taron, daga bisani mataimakin gwamnan jihar, Mani Malam Mummuni, ya jadadda kudirin gwamnatin jihar na siyasa na maido da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.
A cewar sanarwar, yayin taron, mahalarta taron sun tsunduma cikin wani muhimmin nazari kan kalubalen tsaro da ake fama da su tare da daukar sabbin shawarwari guda goma da gwamnatin jihar ta bullo da su.
Ta ce an tsara matakan ne don karfafa nasarorin da aka samu a baya-bayan nan da kuma kara kaimi wajen yaki da ‘yan fashi.
Da yake jawabi, Malam Nakwada ya yabawa jajircewa da sadaukarwar jami’an tsaro da ke aiki a fadin jihar Zamfara.
“Gwamnatin Jiha ta yaba da irin sadaukarwar da ku da manyan jami’an ku suka yi wajen kare lafiyar al’ummarmu, a madadin Mai Girma Gwamna Dauda Lawal, ina mika godiyarmu ga sadaukarwar da kuke yi ba tare da gajiyawa ba.” Inji shi.
SSG ya jaddada bukatar daidaitawa da dabarun hadin gwiwa wajen tinkarar barazanar da ke tasowa, inda ya bayyana cewa, hazaka, kirkire-kirkire, da hadin kai na ci gaba da zama muhimmi wajen samun zaman lafiya mai dorewa.
Ya kara da cewa, “domin tunkarar kalubalen tsaro masu sarkakiya yadda ya kamata, dole ne mu ci gaba da daidaitawa, yin sabbin abubuwa, da kuma yin aiki tare ba tare da wata matsala ba fiye da kowane lokaci.
Malam Nakwada ya kuma bayyana bakin cikinsa kan yawaitar hare-hare a sassan jihar, inda ya mika sakon ta’aziyyar gwamnati ga iyalai da al’ummomin da abin ya shafa.
“A madadin gwamnatin jihar Zamfara, ina jajantawa duk wadanda hare-haren baya-bayan nan ya rutsa da su, ina kuma tabbatar wa ‘yan kasa cewa ba za mu yi kasa a gwiwa ba har sai an samar da cikakken zaman lafiya a tsakanin kowace al’umma,” inji shi.
Ya kuma kara nanata kudirin Gwamna Dauda Lawal na samar wa jami’an tsaro kayan aiki, da tallafin da ake bukata domin fatattakar masu aikata miyagun laifuka da ke barazana ga zaman lafiya da tsaro a jihar Zamfara.
A nasa jawabin rufe taron mataimakin gwamna Mani Malam Mummuni ya yaba da gudunmawar da masu ruwa da tsaki suka bayar tare da yin kira da a kara himma da hadin kai.
“Muna matukar godiya da kokarin da aka yi ya zuwa yanzu, amma dole ne mu kara himma. Bari mu tabbatar da kowane inci na jihar mu da muke so mu maido da fata ga jama’armu,” in ji shi.
Taron dai wani mataki ne mai jajircewa da gwamnatin Dauda Lawal ta dauka na magance matsalolin tsaro a gaba, yayin da gwamnatin ke kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Zamfara.
REL/AMINU DALHATU