Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule Lamido
Published: 23rd, July 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya zargi Shugaba Bola Tinubu da amfani da hukumomin gwamnati wajen danne ’yan adawa.
Ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi da manema labarai a Kano.
Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa An kone babur din ‘barayin waya’ a KanoLamido, ya ce hukumomi irin su EFCC ana amfani da su ne wajen matsa wa ’yan adawa lamba.
Ya bayar da misalin tsohon Gwamnan Delta, Ifeanyi Okowa, wanda ke fuskantar tuhuma kan zargin aikata almundahana.
A cewarsa bayan Okowa ya koma jam’iyyar APC, an daina tuhumarsa.
Ya kafa misali da wata magana da Sanata Adams Oshiomhole ya taɓa yi.
Ya ce: “Da zarar ka shiga APC, an yafe maka zunubanka.” (Ko da yake Oshiomhole ya musanta yin wannan magana).
Lamido, ya gargaɗi gwamnati cewa amfani da ƙarfin iko wajen azabtar da ’yan adawa zai zama barazana ga dimokuraɗiyya.
Ya ce yanzu Najeriya na fama da rashin tsaro, rarrabuwar kawuna da rashin amana, wanda shi ne abin da ya fi dacewa gwamnati ta mayar da hankali a kai.
Ya kuma soki yunƙurin da ake yi na kafa jam’iyyar haɗaka kafin zaɓen 2027.
Lamido, ya ce duk wani yunƙuri na kafa sabuwar ƙungiya ya zama wajibi ya dogara da manufofi masu amfani kamar dimokuraɗiyya, zaman lafiya, tsaro da cibgaban ƙasa, ba kawai burin mulki ko ramuwar gayya ba.
Duk da matsalolin da PDP ke fuskanta, Lamido, ya ce har yanzu yana da kishin jam’iyyar.
Amma ya ƙara da cewa, matuƙar PDP ba za ta samar da abin da ake so, zai mara wa wasu muddin hakan zai amfani ƙasa.
Game da zargin cewa yana yi wa jam’iyyar adawa aiki, Lamido ya ce: “Ina ƙoƙari ne na dawo da jam’iyyar PDP kan turbar da ta dace.”
Ya kuma zargi wasu gwamnonin PDP da yin aiki da Tinubu a ɓoye ba tare da an hukunta su ba.
Ya ce PDP sai ta dawo kan tsarin gaskiya, adalci da dimokuraɗiyya idan tana so ta dawo da ƙarfinta.
“Ƙasar nan na cikin matsala ga yunwa, talauci, da rashin tsaro sun yawaita,” in ji shi.
Game da batun ƙirƙiro sabbin jihohi, Lamido, ya ce wannan ra’ayi yana da kyau amma ba yanzu ne lokacin da ya dace a bijiro da shi ba.
Ya ce ya fi dacewa a mayar da hankali kan warware matsaloli kamar rashin tsaro da yunwa.
Da aka tambaye shi game da ziyarar jagoran NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya kai wa Shugaba Tinubu, Lamido, ya ce bai da abin cewa.
“Kwankwaso da Tinubu na da ‘yancin su gana. Ku tambaye shi da kanku,” in ji shi.
A ƙarshe, Lamido, ya ce mafitar Najeriya na cikin dawo da amana, gaskiya, da bin doka a harkokin siyasa da gwamnati.
“Ina tare da PDP ɗari bisa ɗari, amma idan mafita ga Najeriya tana wajen PDP, zan bi ta domin Najeriya ta fi komai muhimmanci,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Adawa Kwankwaso Tsara yunwa
এছাড়াও পড়ুন:
Chadi: Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa
Majalisar dokokin kasar Chadi ta amince da gyare-gyaren kundin tsarin mulkin kasar da zai tsawaita wa’adin shugabancin kasar daga shekaru biyar zuwa bakwai da kuma baiwa shugaban kasar damar ci gaba da mulki na tsawon wa’adi maras iyaka.
Majalisar dokokin kasar Chadi ta amince da sabon kundin tsarin mulkin kasar a ranar Litinin da kuri’u 171, yayin da aka kada kuri’a daya tilo da taki amincewa da hakan.
A ranar 13 ga watan Oktoba ne aka shirya kada kuri’ar karshe a majalisar dattawa, a cewar sanarwar da shugaban majalisar Ali Koloto Chaimi ya fitar, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Reuters ya ruwaito. Sannan kuma shugaban kasar zai sanya hannu kan kundin tsarin mulkin sannan ya zama doka.
Shugaban kasar Chadi, Mahamat Idriss Deby ya karbi mulkin kasar ne bayan kisan mahaifinsa tsohon shugaba Idriss Deby, a lokacin da ya ziyarci sojojin da ke yaki da mayakan ‘yan tawaye a arewacin kasar a shekarar 2021.
Deby ya yi ikirarin samun nasara bayan zaben da aka gudanar bayan shekaru uku na mulkin soja a watan Mayun 2024, sannan kuma aka gudanar da zaben ‘yan majalisar dokoki a watan Disamba, wanda ya bai wa jam’iyya mai mulki rinjayen kujeru.
An samu cece-kuce game da sakamakon zaben, bayan da madugun ‘yan adawa kuma firaministan kasar Succe Massara ya yi ikirarin samun nasara, ikirarin da hukumar zaben kasar ta yi watsi da shi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci