APC Ta Zabi Kamilu Sa’idu A Matsayin Dan Takarar Kaura Namoda Ta Kudu A Zamfara
Published: 22nd, July 2025 GMT
Jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara ta zabi Hon. Kamilu Sa’idu (Wamban Kasuwar Daji) a matsayin dan takararta na Majalisar Dokokin Jihar Kaura Namoda ta Kudu da za a yi ranar 16 ga Agusta, 2025.
A wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Yusuf Idris Gusau ya fitar, ya ce Kamilu ya fito ne ba tare da hamayya ba bayan janyewar wasu ‘yan takara uku Bashir Muhammad Madaro (Walin Kurya), Anas S/Fada, da Alhaji Ashiru Hamisu Habibu—a lokacin zaben fidda gwani na jam’iyyar da aka gudanar a makarantar firamare ta Kasuwar Daji.
Sanarwar ta ce, ‘yan takarar ukun sun sauka ne domin nuna goyon bayansu ga Kamilu Sa’idu inda suka yi alkawarin samun nasararsa da na jam’iyyar a zabe mai zuwa.
Ta ce an zabo wakilai 30 daga gundumomi shida na mazabar Kagara, Dan-Isa, Sakajiki, Kurya, Kyambarawa, da Banga — ya tabbatar da takararsa gaba daya.
Kwamitin zaben fidda gwani na jam’iyyar APC na kasa, karkashin jagorancin Barista Babande B. Imam ne ya jagoranci gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyar, wanda a hukumance ya ayyana Kamilu Sa’idu a matsayin dan takarar jam’iyyar APC bayan da wakilan unguwanni suka amince da shi.
Barista Babande ya bayyana cewa dan takarar ya cika dukkan sharuddan tsarin mulki na jam’iyyar, kuma an tabbatar da shi a gaban jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), karkashin jagorancin kwamishina Dr. Muhammad Isah.
Bayan wannan sanarwa, shugaban kwamitin shari’a, Isah Halilu Ahmad, ya bayyana cewa idan akwai wani mai korafi dangane da sakamakon zaben fidda gwani ya fito yayi, kuma ba a sami wand ya gabatarda wani korafi ba domin duka masu neman takara da wakilai sun tabbatar da gamsuwarsu da tsarin.
Daga nan sai ya tabbatar da cewa an gudanar da zaben cikin gaskiya da adalci, ba tare da wani magudi ba.
An gudanar da zagaye da manyan jagororin jam’iyyar da suka hada da shugaban jam’iyyar APC na jihar Zamfara, Hon. Tukur Umar Danfulani; Sakataren, Hon. Ibrahim Umar Dangaladima; Mataimakin shugaban kungiyar Alh. Hassan Marafa Damri da halartar jami’an tsaro da jami’an INEC.
REL/AMINU DALHATU.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Zamfara zaben fidda gwani jam iyyar APC na jam iyyar tabbatar da jam iyyar a
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta dakatar da babban taron PDP
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta dakatar da jam’iyyar PDP daga gudanar babban taronta na ƙasa da aka shirya yi a Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, a watan gobe.
Mai shari’a James Omotosho ne, ya bayar da wannan umarni, yayin da yake yanke hukunci kan wata ƙara da aka shigar domin sanin ko jam’iyyar PDP na da ikon ci gaba da shirya taron da aka tsara gudanarwa a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba.
Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4mWaɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Austine Nwachukwu, shugaban PDP na Jihar Imo; Amah Abraham Nnanna, shugaban PDP na Jihar Abiya da Turnah George, sakataren PDP na yankin Kudu maso Kudu.
Waɗanda ake ƙarar sun haɗa da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), PDP, Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Samuel Anyanwu, Sakataren shirya taruka na jam’iyyar, Umar Bature, Kwamitin Ayyuka na jam’iyyar na Ƙasa (NWC) da Kwamitin Zartarwa na jam’iyyar na Ƙasa (NEC).
Masu shigar da ƙarar sun kasance ’yan tsahin Nyesom Wike ne.
Sun roƙi kotu da ta hana gudanar da taron, inda suka bayyana cewar jam’iyyar ta saɓa wa dokokinta, Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999, da kuma Dokar Zaɓe wajen shirya taron.
Lauyansu ya shaida wa kotu cewa: “Ba a gudanar da taron wakilai a jihohi 14 ba don haka shirin taron ya saɓa wa doka.”
Sai dai PDP ta kare kanta, inda ta ce lamarin na harkokin cikin gidan jam’iyyar ne, don haka bai kamata kotu ta tsoma baki ba.
Jam’iyyar ta zargi masu ƙarar da ƙoƙarin tayar da rikici domin hana ta gudanar da sabon zaɓen shugabanni.
Aminiya ta ruwaito cewa wannan rikici ya ƙara dagula al’amura a jam’iyyar PDP.
Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, a baya ya yi zargin cewa an yi amfani da hannunsa na bogi a takardun da aka aike wa INEC game da shirya taron.
Amma shugabancin jam’iyyar ya ƙaryata wannan zargi.
A halin yanzu, Kwamitin Shirya Taron na Ƙasa (NCOC) ya ɗage tantance ’yan takara da aka tsara gudanarwa a ranar 28 ga watan Oktoba.
Mutane da dama na ganin ɗage tantance ’yan takarae na da nasaba da jiran sakamakon hukuncin kotu kafin a ci gaba da shirye-shirye.