Jam’iyyar APC reshen jihar Zamfara ta zabi Hon. Kamilu Sa’idu (Wamban Kasuwar Daji) a matsayin dan takararta na Majalisar Dokokin Jihar Kaura Namoda ta Kudu da za a yi ranar 16 ga Agusta, 2025.

 

A wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar APC na Jihar, Yusuf Idris Gusau ya fitar, ya ce Kamilu ya fito ne ba tare da hamayya ba bayan janyewar wasu ‘yan takara uku Bashir Muhammad Madaro (Walin Kurya), Anas S/Fada, da Alhaji Ashiru Hamisu Habibu—a lokacin zaben fidda gwani na jam’iyyar da aka gudanar a makarantar firamare ta Kasuwar Daji.

 

Sanarwar ta ce, ‘yan takarar ukun sun sauka ne domin nuna goyon bayansu ga Kamilu Sa’idu inda suka yi alkawarin samun nasararsa da na jam’iyyar a zabe mai zuwa.

 

Ta ce an zabo wakilai 30 daga gundumomi shida na mazabar Kagara, Dan-Isa, Sakajiki, Kurya, Kyambarawa, da Banga — ya tabbatar da takararsa gaba daya.

 

Kwamitin zaben fidda gwani na jam’iyyar APC na kasa, karkashin jagorancin Barista Babande B. Imam ne ya jagoranci gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyar, wanda a hukumance ya ayyana Kamilu Sa’idu a matsayin dan takarar jam’iyyar APC bayan da wakilan unguwanni suka amince da shi.

 

Barista Babande ya bayyana cewa dan takarar ya cika dukkan sharuddan tsarin mulki na jam’iyyar, kuma an tabbatar da shi a gaban jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), karkashin jagorancin kwamishina Dr. Muhammad Isah.

 

Bayan wannan sanarwa, shugaban kwamitin shari’a, Isah Halilu Ahmad, ya bayyana cewa idan akwai wani mai korafi dangane da sakamakon zaben fidda gwani ya fito yayi, kuma ba a sami wand ya gabatarda wani korafi ba domin duka masu neman takara da wakilai sun tabbatar da gamsuwarsu da tsarin.

 

Daga nan sai ya tabbatar da cewa an gudanar da zaben cikin gaskiya da adalci, ba tare da wani magudi ba.

 

An gudanar da zagaye da manyan jagororin jam’iyyar da suka hada da shugaban jam’iyyar APC na jihar Zamfara, Hon. Tukur Umar Danfulani; Sakataren, Hon. Ibrahim Umar Dangaladima; Mataimakin shugaban kungiyar Alh. Hassan Marafa Damri da halartar jami’an tsaro da jami’an INEC.

 

REL/AMINU DALHATU.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara zaben fidda gwani jam iyyar APC na jam iyyar tabbatar da jam iyyar a

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano

Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa (NHIA) a ranar Laraba ta kaddamar da shirin bayar da kulawar lafiyar gaggawa kyauta ga yara a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH), Kano.

Shirin, a cewar Darakta a hukumar, Dr. Salahudeen Sikiru, wani bangare ne na fadada shirin lafiyar iyaye da NHIA ke aiwatarwa zuwa ga yara masu rauni da masu bukata ta musamman.

Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono

Ya ce an fara shirin fiye da shekara ɗaya da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai ’yan kasa da shekaru biyar.

“Mun fara wannan shiri fiye da shekara guda da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai. Yanzu mun zo nan don fara na ɓangaren jarirai. Mu za mu biya kudin kulawar gaggawar yaran sannan mu tabbatar an kula da su har su samu ingantacciyar lafiya,” in ji Dr. Sikiru.

Ya kuma ce a karkashin shirin, yara da ke fama da matsalolin gaggawa kamar rashin numfashi, amosanin jini, cutar shawara da yaran da aka haifa bakwaini da ma cututtukan da ke buƙatar tiyata za su samu kulawa kyauta.

Ya ce asibitoci za su fara ba da kulawa da zarar an kawo yara, sannan su tura adadin kuɗin kula da yaran a kowanne mako ga NHIA don a biya su.

Daraktan ya kara da cewa duk yaran da ya sami kulawar gaggawar kuma, za a saka shi cikin shirin inshorar lafiya na NHIS, inda hukumar za ta ci gaba da biyan kudin inshorar don tabbatar da samun kulawar lafiya mai inganci.

“Kafin yaro ya ci gajiyar shirin, dole ne a tantance shi a a tabbatar yana da rauni da kuma ba zai iya biyan kuɗin asibiti ba. Haka nan dole ne yaro ya mallaki Lambar Shaida ta Kasa (NIN) don tabbatar da gaskiya da shigar da su cikin tsarin,” in ji shi.

Dr. Sikiru ya kuma ce, “Shiri ne kula da marasa lafiya cikin gaggawan. Da zarar sun zo, za a duba su. Asibitin sai ya turo mana jimillar adadin kudin, mu kuma mu biya.”

Ya ce wannan shiri wani bangare ne na kudurin gwamnatin tarayya na rage mace-macen jarirai da tabbatar da cewa babu yaron da ya rasa kulawar asibiti saboda rashin kudi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • Bida Poly ta kawo sojoji su kula da jarrabawar ɗalibai
  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba