Aminiya:
2025-07-25@00:38:39 GMT

WFP zai dakatar da tallafin abinci da kiwon lafiya a Nijeriya

Published: 23rd, July 2025 GMT

Shirin Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana cewa daga ƙarshen watan Yuli, zai dakatar da tallafin gaggawa na abinci da kiwon lafiya ga mutum miliyan 1.3 a Arewa maso Gabashin Nijeriya saboda ƙarancin kuɗi.

Darektan WFP a Nijeriya, David Stevenson, ya ce kayan abinci da na kiwon lafiya sun ƙare gaba ɗaya, kuma rabon da ake yi yanzu shi ne na ƙarshe.

Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi 2027: Obi zai iya takara ba tare da ni ba — Datti Baba-Ahmed

Ya ce tallafin zai tsaya ne daga ƙarshen watan Yuli, lokacin da aka ƙiyasta kayan abinci da na kiwon lafiyar za su ƙare gaba ɗaya.

Idan ba a samu tallafi cikin gaggawa ba, mutane da dama za su fuskanci yunwa, gudun hijira ko kuma shiga hannun ‘yan tayar da ƙayar baya.

A cewar Mista Stevenson, kusan mutum miliyan 31 ke fama da matsananciyar yunwa a ƙasar wanda shi ne mafi muni a tarihi.

“Yara ƙanana za su fi shan wahala, domin fiye da asibitoci 150 a Borno da Yobe da ke kula da yara ’yan ƙasa da shekaru biyu za su rufe,” in ji daraktan.

WFP na buƙatar dala miliyan 130 domin cigaba da ayyukanta har zuwa ƙarshen shekarar 2025.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da tashe-tashen hankula ke ƙaruwa, kuma yunwa na kai matsayi mafi muni a tarihin ƙasar

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas Majalisar Ɗinkin Duniya Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano

An shawarci mata da su daina amfani da tsumma ko soson katifa, da takarda a lokacin al’adar su don inganta tsafta da rigakafin matsalolin lafiya.

 

Jami’ar tallafawa masu kula da tsaftar jinin haila a jihar Kano (MH-NoW) Amina Sabiu Musa ta yi wannan kiran ne a lokacin wani taron karawa juna sani na tsaftar jinin haila ga kwararrun ‘yan jarida da masu fada a ji a shafukan sada zumunta da aka gudanar a Kano.

 

A cewarta, shirin na MH-NoW ya shafi ‘yan mata da mata masu shekaru 10 zuwa 24 su 200,000 da nufin magance matsalar talaucin kudin sayen audugar mata a fadin Najeriya.

 

Ta bayyana cewa shirin wanda Population Services International (PSI) Nigeria ta aiwatar, zai hada da masu raba kayan aikin tsaftar muhalli da za a sake amfani da su don taimakawa wajen rage radadin talauci a wannan banagen.

 

“Ana gudanar da aikin a wasu jahohin Najeriya, tare da mai da hankali kan dalibai da mata matasa a al’ummomi 15 dake fadin kananan hukumomin Ghari, Tsanyawa, da Nasarawa a Kano,” in ji Amina.

 

Shima da yake jawabi a wajen taron, mataimakin daraktan bincike da kididdiga na ma’aikatar mata, yara da masu bukata ta musamman ta jihar Kano, Alhaji Zubair Abdulmumin Zubair ya bukaci iyaye da su ba da fifiko ga tsaftar jinin haila ta hanyar samar da kayan tsafta da kuma jagoranci mai kyau ga ‘ya’yansu mata.

 

Ya nuna damuwarsa kan rahotannin da ke cewa dalibai mata da yawa ba sa zuwa makaranta a lokutansu sakamakon rashin samun kayayyakin tsaftar muhalli da kuma rashin audugar mata a lokacin al’ada.

 

Ya yi kira ga maza, iyaye, maza da mata da duk masu ruwa da tsaki da su yi watsi da tatsuniyoyi masu cutarwa game da jinin haila tare da tallafawa ilimin haila.

 

“Dole ne kuma a ilmantar da maza game da jinin haila don su fahimci sauyin yanayi da yanayin da mata ke fuskanta a lokacin al’ada,”

 

Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da gidan rediyon Najeriya Aminu Abdullahi da Hannatu Sulaiman Abba da kuma Maimuna O. Yusuf sun bayyana taron da ya dace.

 

A matsayinsu na masu yada labarai, sun yi alkawarin ba da horo ga wasu kuma za su yi amfani da dandamali daban-daban na don Magana akan haila.

 

 

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa taron bitar ya samu halartar dimbin mahalarta.

 

Khadija Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya fi mayar da hankali wajen gina Kudancin Nijeriya — Kwankwaso
  • Fiye Da  Falasdinawa 111 Ne Su Ka Yi Shahada Saboda Yunwa A Gaza
  • Ministan Lafiya Na Kamaru: Hadin-Gwiwa Ta Fuskar Kiwon Lafiya Ta Shaida Zumunci Mai Karfi Tsakanin Kamaru Da Sin
  •  Fiye Da  Kungiyoyin 100 A Duniya Sun Yi Gargadi Akan Halin Yunwa Da HKi Ta Jefa Mutanen Gaza A Ciki
  • A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24
  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
  • NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa
  • Yunwa na ƙara tsanani a Arewa maso Gabashin Nijeriya — ICRC
  • An kaddamar Da Wani Shiri Na Ba ‘Yan Mata 200,000 Tallafin Audugar Mata A Kano