A dokar hukumar zabe ta 2010 sashe na 124, biyan kudi ga wani a matsayin cin hanci a kowane irin zabe ko karbar kudi ko kyauta domin jefa kuri’a ko hana jefa kuri’a a kowane zabe babban laifi ne da ke da hukuncin tarar naira dubu 500, 000 ko daurin watanni 12 a gidan gyaran hali ko kuma duka biyu.

A kowane zabe kama daga na shugaban kasa zuwa kansila, Hukumar Zabe da hukumomin yaki da cin hanci da rashawa na fuskantar kalubale daga masu sayen kuri’a da ke canzawa masu zabe zaben ra’ayin kan su zuwa zaben wanda aka ba su kudi ko ma kin yin zaben.

Duk da kama masu sayen kuri’a da hukumomin yaki da cin hanci da rashawa ke yi, galibi ba a cika jin sun gurfanar da masu aikata wannan danyen laifin a gaban kotu ba wanda hakan ya yi tasiri wajen ba su damar ci-gaba da cin karen su ba babbaka.

A bisa ga amfani da kudi wajen sayen kuri’u jam’iyyun siyasa da ‘yan takarar su na samun nasarar kayar da nagartattun ‘yan siyasar da ke da ingantattun kudurori da manufofin inganta rayuwar al’umma.

Hukumomin yaki da cin na EFCC da ICPC a kowane zabe kan bayyanawa al’umma illar sayen kuri’a tare da kira ga al’umma da su kwarmata bayanin sayen kuri’a tare da tukaicin samun na goro ga duk wanda ya bayar da rahoton amfani da kudi wajen sayen kuri’a, sai dai duk da hakan matsalar ta’azzara take yi ba raguwa ba.

Hukumar kididdiga ta Nijeriya wato NBS ta tabbatar da cewar an samu yawaitar sayen kuri’a da sayar da ita a babban zaben 2023 da ya gabata a dukkanin zabuka.

A rahoton da hukumar ta fitar kan cin hanci a Nijeriya ta bayyana cewar a zaben 2023 an samu yawaitar sayen kuri’a kashi 22% wanda ya karu sama da kashi 5 a kan na zaben 2019 da kashi 17%.

A cewar NBC a rahoton da ta fitar a Yuli 2023 ‘yan Nijeriya kashi 22% ne suka kai rahoton an ba su kudi domin sayen kuri’un su kafin da yayin zaben 2023, a yayin da kashi 9 aka ba su wasu abubuwan daban

“A 2023 kashi 10 na mutane sun bayyana cewar ba a ba su kudi domin sayen kuri’a ba amma an baiwa wani daga cikin ‘yan gidan su wanda ya wuce na 2019 da kashi 5.

Sai dai hukumar ta bayyana cewar kashi 55 na ‘yan Nijeriya da aka baiwa kudi ko kayan masarufi domin sayar da kuri’a sun bayyana cewar cin hancin bai canza ra’ayin su ba, to amma kashi 40 sun bayyana cewar sun zabi jam’iyya ko dan takarar da ya ba su kudi.

A kan gagarumar matsalar sayar da kuri’a da illar ta ga zabe mai zuwa, tuni masana da masu ruwa da tsaki suka fara kira ga al’umma da su tashi tsaye su yaki matsalar wadda ke hanawa mulkin dimokuradiyya ci-gaba mai ma’ana.

Tsohon Gwamnan jihar Bayelsa kuma Sanatan da ke wakiltar Bayelsa ta Yamma a Majalisar Dattawa, Sanata Henry Seriake Dickson na kan gaba wajen bukatar al’umma da hukumomin da lamarin ya shafa da su daura damarar kawar da matsalar sayen kuri’a da buga sakamakon zaben bogi.

Sanata Dickson ya bayyana hakan ne a bayanin da matainakinsa kan yada labarai a Arewa, Jamilu Abubakar ya fitar yana cewar masu ruwa da tsaki da ‘yan Nijeriya bakidaya suna da hakkin gyara abubuwan maras kyau da ke faruwa a kasar nan.

Tsohon Gwamnan ya ce gurbatattun abubuwan da ke gudana a karkashin jagorancin masu hali da ‘yan siyasa masu fada aji lamari ne da zai tarwatsa tsarin siyasar kasar nan.

Sanatan ya bayyana fatara da rashin sani a matsayin kashin bayan da gurbatattun ‘yan siyasa ke amfani wajen samun kuri’a ta hanyar amfani da kudi da kayan masarufi.

Ya ce wannan matsalar ta jefa ‘yan Nijeriya a cikin kunci da mayar da kasa baya domin mutanen da ba su cancanta ba ke rike da mukamai wadanda babu nauyin da suke saukewa bayan samun nasara.

“Na yi Allah- wadai da amfani da madafun iko da tsara sakamakon zabe kafin zabe ta hanyar amfani da karfin mulki da hukumomi.”

“Wajibi ne Hukumar Zabe ta samu hanyoyin magance wadannan matsalolin a wajen jefa kuri’a maimakon neman hakki a bangaren shari’a wanda daga karshe kotu za ta sanya wasu dubaru ta kori kara mai kyau ta fashin zabe.” Ya bayyana.

Ya ce irin wannan matsalar na samar da mutanen da ba su ko iya cin zabe a cikin dangin su ko al’ummar su amma sune ke tinkahon lashe zabe.

A cewarsa a matsayinsa na dan majalisar dattawa suna kokarin gabatar da dokokin da za su shawo kan wadannan matsalolin, ya ce sun san hukumar zabe ba za ta iya kula da abubuwan da jami’an tsaro ke yi a yayin zabe ba.

“Shi ne dalilin da yasa ake canza sheka zuwa jam’iyya mai mulki domin samun damar amfani da madafun ikon cin zabe ta kowace irin hanya.”

A wani bincike da Cibiyar Ayyukan Majalisa da Dimokuradiyya a Nijeriya ta gudanar ta bayyana cewar sayen kuri’a ya samu gindin zama a farfajiyar siyasar Nijeriya wanda ya kamata a dauki kwakkwaran matakin shawo kan matsalar.

Cibiyar ta bayyana cewar hakan ya faru ne saboda jam’iyyun siyasa da ‘yan takarar su sun nuna a fili a yayin yekuwar neman zabe cewar jam’iyyun da ke da ingantattun manufofi da nagartattun ‘yan takara ba su isa su kadai su tabbatar da nasarar zabe ba wanda shine dalilin da yasa suka zabi sayen kuri’a.

Haka ma su kan su masu zabe sun nuna amincewar a ba su kudi su sayar da ‘yancin su ga wanda zai bada kudi mafi yawa a kowane irin zabe wanda hakan babban kuskure ne da ke haifar da zaben tumun dare.

A binciken da cibiyar ta gudanar ta bayyana cewar sayen kuri’a na yin tasiri kwarai wajen canza ra’ayin masu zabe wanda babban kalubale ne ga dukkanin masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa a Nijeriya musamman hukumar zabe.

Idan har za a gudanar da zaben gaskiya da adalci ya kuma zama mai amfani ga ingantaccen mulki to wajibi ne a yaki matsalar sayen kuri’a kamar yadda cibiyar ta jaddada.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Masu Ruwa Da Tsaki ta bayyana cewar sayen kuri a da yan Nijeriya hukumar zabe

এছাড়াও পড়ুন:

Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista

Ya ce: “Ba mu kai inda muke so ba a fannin tattalin arziki, amma muna iya gani cewa abubuwa suna tafiya a hankali. Shugaban Ƙasa ya faɗa sau da dama cewa mun fara fitowa daga ƙunci.

 

“Na san mutane da yawa za su ce ba mu kai ga cikakken cigaba da jin daɗin tattalin arziki ba tukuna. Gaskiya ne! Ni ma na yarda. Amma ba za mu ce babu cigaba ko kaɗan ba.”

 

Ya ƙara da cewa: “Ko hukumomin ƙididdiga na duniya suna fara ba Nijeriya kyakykyawan matsayi. Muna ganin alamu na ɗagawa a hanyar da ake tafiyar da tattalin arzikin mu.”

 

Idris ya ce manyan matakan sauyi kamar cire tallafin man fetur da daidaita farashin musayar kuɗi suna fara nuna tasiri mai kyau a ƙasar nan.

 

Haka kuma ya bayyana cewa sama da ɗalibai 300,000 ne suke cin gajiyar shirin bayar da rancen karatu na gwamnati, wanda ke ɗaukar nauyin kuɗin makaranta da kuma ciyar da su.

 

Ya ce: “Saboda wannan manufa da aka tsara ta gwamnati, sama da ɗalibai 300,000 na Nijeriya da a da ba za su iya zuwa makaranta ba ko kuma da suka riga suka bar makaranta, yanzu suna da damar komawa makaranta domin gwamnati tana biya masu kuɗin makaranta da na ciyarwa. Ba a taɓa samun irin wannan ba.”

 

A kan batun tsaro, Ministan ya ce gwamnati tana ɗaukar matakai masu ƙarfi don shawo kan matsalolin tsaro, inda ya ce dakarun soji na samun nasarori a yaƙi da masu laifi a sassa daban-daban na ƙasar nan.

 

Ya roƙi kafafen yaɗa labarai da su goyi bayan ƙoƙarin da rundunonin tsaro suke yi, tare da guje wa bai wa masu laifi muhimmanci fiye da kima.

 

“Ina ta faɗa tun da farko cewa ba daidai ba ne mu a matsayin mu na ‘yan jarida mu riƙa ba waɗannan masu laifi, masu tayar da ƙayar baya, ‘yan ta’adda ko ɓarayi ko duk yadda za a kira su, fifiko fiye da ‘yan Nijeriya nagari,” inji shi.

 

Ya ce ya kamata kafafen watsa labarai su riƙa bayyana nasarorin da sojoji suke samu da sadaukarwar su, maimakon maida hankali kawai a kan hare-hare da rashin nasara.

 

Idris ya bayyana cewa ko da yake aikin kafafen watsa labarai ne su riƙa sa ido kan gwamnati ta hanyar suka mai amfani, wajibi ne su kuma riƙa bayyana nasarori da cigaban da ake samu.

 

A martanin sa kan Rahoton Gyaran Dokoki da ƙungiyar ta gabatar, Ministan ya ce zai tattauna da Ministan Shari’a kuma babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, tare da kafa kwamitin musamman a ma’aikatar sa domin nazarin rahoton.

 

Ya jaddada cewa manufar gwamnatin Tinubu tana daga cikin ginshiƙan dimokiraɗiyya ita ce kare ‘yancin faɗar albarkacin baki da ‘yancin kafafen yaɗa labarai.

 

Sai dai ya ja hankalin ‘yan jarida da su riƙa amfani da wannan ‘yanci cikin kishi da kishin ƙasa, tare da riƙon gaskiya da haɗin kai don ci gaban ƙasa.

 

Idris ya taya sababbin shugabannin ƙungiyar murna, tare da bayyana shirin sa na ƙarfafa dangantaka tsakanin gwamnati da kafafen watsa labarai.

 

Tun da farko a jawabin sa, Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Editocin Nijeriya, Dakta Sebastian Abu, ya bayyana cewa tawagar ta kai ziyara ofishin Ministan ne don gabatar da rahoton Kwamitin Sauya Dokokin Ƙungiyar a hukumance.

 

Ya bayyana cewa rahoton ya nuna wasu tsofaffin dokoki a kundin tsarin mulki da suka zama ƙalubale ga ‘yancin aikin jarida a Nijeriya, waɗanda ya dace a duba ko a cire su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Magance Matsalar Yara Da Ba Sa Zuwa Makaranta: Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyarwa A Makarantun Jihar
  • Kamfanonin Jiragen Ruwa Sun Yanke Hulda Da Isra’ila Saboda Matsalar Hare-Haren Kasar Yemen
  • NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta
  • Mayakan Huthi Sun Kara Kai Wasu Hare-Hare da Makamai Masu Linzami Kan BenGurio
  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha
  • Abdullahi Ojlan Ya Sanar Da Kawo Karshen Fada Da Makami
  • Kwanan nan gwamnati za ta sake kara kudin lantarki a Najeriya – Minista
  • Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC