Aminiya:
2025-07-23@10:36:34 GMT

Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare

Published: 23rd, July 2025 GMT

Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Shugaba Bola Tinubu ta karɓo bashin ƙasashen waje da ya haura dala biliyan 21 domin aiwatarwa da cike giɓin kasafin kuɗin shekarar 2025 zuwa 2026.

Majalisar ta bayyana cewa za a yi amfani da bashin ne wajen aiwatar da muhimman ayyukan ci gaban ƙasa, musamman a fannonin ababen more rayuwa, da tsaro, da noma da kuma gina ɗan Adam.

UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 151 a Nijeriya bana — NCDC

Shugaban kwamitin Majalisar Dattawa kan basussukan cikin gida da na waje, Sanata Aliyu Wamako ne ya gabatar da rahoton karbar bashin yayin zaman majalisar a yau Talata.

Sanata Wamakko wanda yake wakiltar shiyyar Sakkwato ta Arewa a zauren majalisar, ya ce an jinkirta amincewar rahoton ne saboda hutu na majalisa da kuma jinkiri wajen samun takardun daga Ofishin Kula da Basussuka (DMO).

Shugaban kwamitin kasafi, Sanata Olamilekan Solomon, ya ce bayyana cewa sahale wa shugaban kasar karbo rancen yana kan tsarin da doka ta bayar da dama kuma tuni an riga an haɗa bashin cikin tsare-tsaren kasafin kuɗi.

Shi ma takwaransa mai wakiltar shiyyar Neja ta Gabas, Sanata Sani Musa, ya bayyana cewa wannan shiri ba na shekara ɗaya ba ne, amma zai shafi rabon kuɗi na tsawon shekara shida, yana mai jaddada cewa Nijeriya ba ta taɓa gazawa wajen biyan bashinta ba.

A nasa bangaren, shugaban kwamitin bankuna da harkokin kuɗi, Sanata Adetokunbo Abiru mai wakiltar shiyyar Legas ta Gabas, ya tabbatar da cewa karbo rancen ya yi daidai da ƙa’idojin dokar kula da bashi da ta ɗabi’un da suka dace da dokar kuɗi.

Sai dai Sanata Abdul Ningi mai wakiltar shiyyar Bauchi ta Tsakiya ya nuna damuwa game da ƙarancin bayanai kan yadda za a raba bashin da kuma hanyoyin da za a biya su.

Ya nemi a bayyana adadin da kowace jiha ko hukuma za ta samu, da kuma amfanin bashin domin a iya bayyana wa al’umma gaskiya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa rance wakiltar shiyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa

Dakatacciyar Sanatar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta lashi takobin sake maka shugabancin Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio a gaban kotun daukaka kara bayan an hana ta shiga harabar majalisar a ranar Talata.

Cikin bacin rai, Natasha ta shaida wa ’yan jarida cewa za ta tattauna da lauyoyinta cikin gaggawa domin fara shigar da karar, tana mai cewa matakin ya saba da hukuncin kotun da ta bayar da umarnin a mayar da ita kan kujerarta.

Lamarin dai ya biyo bayan yadda jami’an tsaron da ke gadin majalisar suka tare hanya suka hana tawagar motocinta shiga majalisar, duk kuwa da umarnin kotu na mayar da ita.

HOTUNA: An ƙaddamar da aikin sabunta ginin Majalisar Dokokin Bauchi Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare

Ta kuma ce hatta dakatar da itan ma da farko ba ya kan ka’ida.

A cewar ta, “Yanzu zan je na tattauna da lauyoyina domin shirin daukaka kara alabasshi kotu ta fassara mana abin da ya faru. Ni mace ce mai bin dokokin kasa.”

Sanatar ta kuma yi alla-wadai da matakin da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio ya dauka na hana ta shigar, inda ta ce hakan tamkar raina kotu ne.

Ta kuma ce, “Akpabio bai fi karfin kundin tsarin mulkin Najeriya ba. Ina so ’yan Najeriya su sani cewa ba Ofishin Shugaban Majalisar Dattawa ne ya mayar da ni Sanata ba.

“Duk da cewa ya tafi daukaka kara, hakan ba yana nufin cewa ya soke hukuncin Mai Shari’a Binta Nyako ba ne kuma hakan ba zai dakatar da ni daga kasancewa Sanata ba.

“Mutanen Kogi ta Tsakiya ne suka zabe ni kuma su nake wakilta,” in ji Natasha.

Tun da farko dai Sanatar ta yi yunkurin shiga majalisar tare da magoya bayanta amma, amma aka hanata, dole sai da ta sauka ta tafi a kafa.

An dai girke tarin jami’an tsaron da ba a saba ganin irin su ba a majalisar, inda aka ga wasu jami’an na duba motoci tare da ma takaita yawan wadanda za su ajiya ababen hawa a wajen fakin na wajen majalisar.

Akalla an ga motocin sintiri na jami’an ’yan sanda guda biyar da aka girke a muhimman wuraren shiga majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • Yanzu-Yanzu: Majalisa Ta Amince Wa Tinubu Ciwo Bashin Dala Biliyan 21
  • Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
  • Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa
  • Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro
  • Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 
  • Kamfanonin lantarki ya zu katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba