Majalisar Dattawa ta sahale wa Tinubu karɓo rancen $21bn a ƙetare
Published: 23rd, July 2025 GMT
Majalisar Dattawa ta amince da buƙatar Shugaba Bola Tinubu ta karɓo bashin ƙasashen waje da ya haura dala biliyan 21 domin aiwatarwa da cike giɓin kasafin kuɗin shekarar 2025 zuwa 2026.
Majalisar ta bayyana cewa za a yi amfani da bashin ne wajen aiwatar da muhimman ayyukan ci gaban ƙasa, musamman a fannonin ababen more rayuwa, da tsaro, da noma da kuma gina ɗan Adam.
Shugaban kwamitin Majalisar Dattawa kan basussukan cikin gida da na waje, Sanata Aliyu Wamako ne ya gabatar da rahoton karbar bashin yayin zaman majalisar a yau Talata.
Sanata Wamakko wanda yake wakiltar shiyyar Sakkwato ta Arewa a zauren majalisar, ya ce an jinkirta amincewar rahoton ne saboda hutu na majalisa da kuma jinkiri wajen samun takardun daga Ofishin Kula da Basussuka (DMO).
Shugaban kwamitin kasafi, Sanata Olamilekan Solomon, ya ce bayyana cewa sahale wa shugaban kasar karbo rancen yana kan tsarin da doka ta bayar da dama kuma tuni an riga an haɗa bashin cikin tsare-tsaren kasafin kuɗi.
Shi ma takwaransa mai wakiltar shiyyar Neja ta Gabas, Sanata Sani Musa, ya bayyana cewa wannan shiri ba na shekara ɗaya ba ne, amma zai shafi rabon kuɗi na tsawon shekara shida, yana mai jaddada cewa Nijeriya ba ta taɓa gazawa wajen biyan bashinta ba.
A nasa bangaren, shugaban kwamitin bankuna da harkokin kuɗi, Sanata Adetokunbo Abiru mai wakiltar shiyyar Legas ta Gabas, ya tabbatar da cewa karbo rancen ya yi daidai da ƙa’idojin dokar kula da bashi da ta ɗabi’un da suka dace da dokar kuɗi.
Sai dai Sanata Abdul Ningi mai wakiltar shiyyar Bauchi ta Tsakiya ya nuna damuwa game da ƙarancin bayanai kan yadda za a raba bashin da kuma hanyoyin da za a biya su.
Ya nemi a bayyana adadin da kowace jiha ko hukuma za ta samu, da kuma amfanin bashin domin a iya bayyana wa al’umma gaskiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa rance wakiltar shiyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.
Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.
Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.
A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.
“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA