Kungiyoyin agaji da kuma na hakkokin bil’adama sun yi gargadi akan yunwar da ake fama da ita a Gaza, tare da yin kira ga gwamnatoci da su yin matsin lamba domin kawo karshe killace Gaza da aka yi, da kuma shigar da kayan agaji a cikin yanki.

Kungiyoyin sun kuma dorawa HKI alhakin halin da mutanen Gaza suke ciki na yunwa.

Daga cikin kungiyoyin da su ka fitar da bayani da akwai Majalisar ‘yan gudun hijira ta kasar Norway” da “Refugee International” da wasu da adadinsu ya kai 111, sun yi gargadi akan yadda yunwa take yaduwa a cikin Gaza.

Bayanin ya kunshi cewa; Mazauna yankin Gaza suna fama da yunwa saboda killace su da Isra’ila ta yi, kuma a duk lokacin da mutanen su ka nunfi wurin da aka ware domin raba abinci sai a bude musu wuta.

Wuararen raba abincin da suke a cikin yankin Gaza dai, HKI da Amurka su ka shriya su a matsayin tarkon kashe Falasdinawa da suke zuwa wurin.

Bayanin ya kuma ce, da akwai kayan abinci, ruwa da magunguna masu yawan gaske da aka ajiye da su a wajen yankin Gaza, amma kuma Isra’ila  ta hana a shiga da su.

Haka nan kuma sun bayyana cewa; Dukkanin kayan agajin da ake da su, sun kare baki daya, kuma kungiyoyin agaji suna Kallon yadda ‘yan’uwansu suke ramewa da kama hanyar mutuwa saboda rashin abinci.

Har ila yau sun yi ishara da cewa: Dokoki da Isra’ila ta kafa ne, da su ka jawo jinki, da kuma yadda take karkatsa yankin na Gaza wanda yake a killace, su ne su ka  haddasa yunwa da mutuwa.”

 Haka nan kuma wadannan kungiyoyin sun yi kira ga gwamnatoci da su kawo karshen bin matakai na cike-ciken takardu akan dukkanin hanyoyi, saboda share fagen shigar da kayan abinci cikin  yankin Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yankin Gaza

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.

 

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.

 

Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin
  • Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000