Lakurawa sun kashe ’yan sanda 3 a Kebbi
Published: 12th, July 2025 GMT
’Yan ta’addan Lakurawa sun karbe ’yan sanda uku har lahira a yankin Gozirma da ke Ƙaramar Hukumar Bunza a Jihar Kebbi.
’Yan sandan sun kwanta dama ne a yayin musayar wuta a yayin da ’yan ta’addan da ke ƙoƙarin kai hari ga matafiya a kan Babbar hanyar Gozirma zuwa Till.
Kakakin ’yan sanda a Jihar Kebbi, ya sanar da cewa a yayin ƙazamin faɗan, “an kashe ’yan ta’adda da dama, amma wasu sun tsere da raunukan harbi a jikinsu.
Ya ƙara da cewa Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kebbi, Bello M Sani, ya yaba da namijin ƙoƙarin jami’an rundunar da ke yankin Zurmi da suka kai wa matafiyan ɗauki.
Direba ya tsere da buhun masara 463 Ɗalibi ya ƙone budurwarsa mai tsohon ciki har lahiraYa yi musu addu’ar samun rahama tare da kiran jama’a da su kwantar da hankali su ci gaba da harkokinsu.
Ya kuma buƙaci su kai wa cibiyar jami’an tsaro mafi kusa rahoton duk wanda suka gani da raunin harbi ko wani take-taken da ba su aminta da shi ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama mutum 98 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban, ciki har da fashi da makami, safarar miyagun ƙwayoyi, sata, zamba da kuma tayar da hankalin jama’a.
An kama waɗannan mutane ne ƙarƙashin sabon samamen da rundunar ta ƙaddamar mai suna “Operation Kukan Kura” wanda ya fara aiki a ranar 1 ga watan Yuli, 2025.
Kotun ƙoli ta tabbatar da Okpebholo a matsayin gwamnan Edo Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawaKwamishinan ’Yan Sandan Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Bompai a ranar Alhamis.
Ya ce wannan aiki wani ɓangare ne na ƙoƙarin daƙile aikata laifuka da tabbatar da zaman lafiya a faɗin Jihar Kano.
Ya ce samamen ya samu goyon bayan Sufetan Janar na ’Yan Sanda, Kayode Adeolu Egbetokun, domin ƙarfafa haɗin kai da al’umma wajen yaƙi da laifuka.
Kwamishinan, ya bayyana cewa wannan aiki yana bin tsarin aikin rundunar, wanda ke nufin haɗa kai da al’umma wajen hana aikata laifuka.
Rundunar ta nazarci halin tsaro a jihar tare da duba yankunan da laifuka suka fi yawa kafin ta ƙaddamar da samamen.
Ya ce babban burin wannan aiki shi ne zama tamkar wata hanyar gargaɗi domin gano da kuma daƙile barazanar laifuka tun kafin su faru.
Daga cikin waɗanda aka kama akwai mutum 21 da ake zargi da fashi da makami, huɗu ana zargin su da garkuwa da mutane, biyar kan safarar miyagun ƙwayoyi.
Sauran sun haɗa da mutum 12 da ake zargi da satar motoci, huɗu ana zargin su da zamba, sai wasu biyar da ake zargi da sata, da kuma mutum 47 da ake zargi da tayar da hankalin jama’a.
Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da motoci guda shida, adaidaita sahu guda takwas, babura guda tara, tabar wiwi, kwalabe 86 na kayan maye, takubba 16 da wuƙaƙe.
Kwamishinan, ya ce waɗannan nasarori za a ci gaba da amfani da su wajen inganta dabarun aiki da rundunar ke aiwatarwa.
Ya ƙara da cewa rundunar za ta ci gaba da ɗaukar matakan kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano.