HausaTv:
2025-07-25@00:34:08 GMT

Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman

Published: 23rd, July 2025 GMT

Sojojin ruwan Iran sun sanar da cewa, wani jirgin ruwan Amurka na yaki da ya yi kokarin shiga tekun Oman, ya fuskanci gargadi daga sojojin ruwan Iran tare da tilasta masa janyewa.

Da saiyar yau Laraba ne dai jirgin sama mai saukar angulu mallakin sojojin ruwa, ya yi gargadi ga jirgin ruwan na Amurka da a karshe ya tilasta masa janyewa.

Da fari, jirgin ruwan yakin na Amurka ya yi wa jirgin sama mai saukar angulu na Iran barazanar kai masa hari, said ai duk da haka sojojin ruwan na Iran sun ci gaba da yin gargadi ga Amurkawan da su kar su shiga cikin ruwan tekun Oman.

Bayan wannan barazana ne aka aikewa jirgin ruwan Amurkan sako daga dakarun  tsaron sararyin samaniyar Iran  akan cewa, wannan jirin mai saukar angulu  yana da cikakkiyar kariya, don haka wajibi ne ga jirgin ruwan na Amurka mai suna “DDG Fitzgerald  ya janye.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jirgin ruwan

এছাড়াও পড়ুন:

Eritrea ta gargadi Habasha game da yunkurin kafa tashar jiragen ruwa a cikin yankinta

Wata sabuwar tashin-tashina ta sake kunno kai a yankin kahon Afirka a daidai lokacin da shugaban kasar Eritrea Isaias Afwerki ya yi gargadi kai tsaye ga firaministan Habasha Abiy Ahmed, inda ya yi kashedin sake kaddamar da wani yaki.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasar Habasha ke kokarin shiga bangaren ruwa Eritra da kuma tabarbarewar dangantakar bangarorin biyu tun bayan rikicin Tigray.

A cikin wani jawabi da ya yi ta gidan telebijin, shugaba Afwerki ya yi gargadin cewa adadin yawan jama’ar Habasha ba zai tabbatar da nasarar soji ba, yana mai nuni da dabarun yakin da  Habasha ta yi amfani da su a yakin da ya gabata, yana mai cewa duk da yawan sojojinta amma bata samu nasara ba.

Afwerki ya kira matakin na Abiy a matsayin “rashin hankali” tare da danganta hakan da matsalolin siyasar cikin gidan Habasha. Ya kuma nanata cewa Eritrea ba za ta amince da keta hurumin kasarta ba, ya kuma bukaci Habasha da ta warware matsalolin cikin gida kafin ta yi la’akari da daukar mataki a kan  waje.

Kasar Habasha wadda ita ce kasa mafi yawan al’umma a gabashin nahiyar Afirka, ta dade tana neman shiga Tekun Bahar Maliya, ayyin da Eritiriya take yin matukar kaffa-kaffa da wannan manufa ta Habasha.

Kasashen Eritrea da Habasha sun jima suna zaman doya da manja tun bayan da Eritrea ta kwashe shekaru 30 tana yakin neman ‘yencin kai da mulkin Habasha, wanda ya kai ga samun ‘yancin kai a 1993.

Rikicin da ya fi kamari ya faru ne daga 1998 zuwa 2000, lokacin da wani mummunan yakin kan iyaka ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 100,000. Duk da yarjejeniyar zaman lafiya da aka sanya hannu a kanta a cikin 2018, amma babu wani tabbaci kan ci gaba da wanzuwar wannan yarjejeniya.

Habasha tana da yawan jama’a miliyan 130, Eritrea miliyan 3.5 kawai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  An Jikkata  Sojojin Sahayoniya 9 Ta Hanyar Take Su Da Mota
  • Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12
  • Yan Majalisar Dokokin Kasashen Iran Da Iraki Sun Amince Da Ra’yin Ficewar Sojojin Amurka Daga Iraki
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • Eritrea ta gargadi Habasha game da yunkurin kafa tashar jiragen ruwa a cikin yankinta
  •  Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta
  • Jihohin da za a samu ruwan sama da iska mai ƙarfi a sassan Nijeriya — NiMet
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila