Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar ya bayyana hukumar kula da shige da fice ta Najeriya a matsayin matakin farko na tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyi a kasar.

 

Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakuncin daliban jami’ar Immigration da ma’aikatan kwalejin Sokoto a ziyarar ban girma a fadarsa.

 

Ya yi kira da a samar da jami’an shige-da-fice don duba bakin haure da ke barazana ga zamantakewa da ci gaban tattalin arzikin kasar.

 

Ya kara da cewa galibin ‘yan kungiyoyin ta’addanci irin su Lakurawas da Boko Haram ba ’yan Najeriya ba ne.

 

Jagoran ya bayyana cewa, hukumar shige da fice na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da tsaron kasa ta hanyar amfani da bayanan sirri, tantancewa da kuma yin tambayoyi domin gano tare da kama mutanen da ke da tarihin aikata laifuka, da ‘yan ta’adda, ko kuma wadanda ke haifar da wasu matsalolin tsaro kafin samun damar shiga yankunan kasar.

 

Jagoran ya kara da cewa, Mai Alframa Sarkin Musulmi a shirye yake a kodayaushe don tallafa wa dukkanin hukumomin gwamnati da ke da alaka kai tsaye ga zamantakewa da tattalin arzikin kasa.

 

A farkon jawabinsa, mukaddashin kwamandan hukumar kula da shige da fice da ma’aikata ta kwalejin Sokoto Muhammad Mu’azu ya ce makasudin ziyarar shi ne mika godiya da kuma samun nasiha ta uba daga mai Alframa Sarkin Musulmi .

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Sakkwato Sarkin Musulmi

এছাড়াও পড়ুন:

Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa

Wasu kudurori guda 3 da ke dauke da bukatun kafa wasu hukumomi 3 sun samu karatu na biyu a zauren majalaisar dokokin jihar Jigawa.

Kudurorin guda 3 sun hada da na kafa Hukumar Samar da Hanyoyin Mota a yankunan karkara, da na kafa Hukumar Samar da Kudade Domin Ayyukan Hanyoyin Mota a yankunan karkara da Kuma na Hukumar Bunkasa Kwazon Malamai ta jihar Jigawa.

A lokacin ya ke gabatar da kudurorin domin neman goyon baya kan bukatar kafa hukumar bunkasa kwazon malamai, mataimakin shugaban masu rinjaye na majlaisar, Alhaji Sani Sale Zaburan ya ce gwamnatin jihar na da nufin inganta aikin koyarwa ta hanyar kafa hukumar da za ta rinka horas da malamai akai akai.

Da su ke tattaunawa kan wannan batu, wakilan mazabar Kanya Babba da na Fagam da na Sule Tankarar da na Guri, sun lura cewa kafa wannan hukumar zai maye gurbin ayyukan kwalejin horas da malamai da aka rushe a can baya, abin da zai kawo ingancin harkonin koyo da koyarwa a halin yanzu.

Kazalika da ya ke gabatar da kudurin neman goyon baya kan batun kafa hukuma da kuma asusun samar da hanyoyin mota a yankunan karkara, mataimakin shugaban masu rinjaye na majalisar, Alhaji Sani Sale Zaburan ya ce daukar wannan mataki zai karfafa yunkurin gwamnatin jihar na inganta harkokin sufuri ga jama’ar karkara.

Da su ke bada gudummawa kan wannan batu, wakilin mazabar Gwaram da na Kiri Kasamma da na Guri da kuma wakilin mazabar Fagam sun bayyana kudurorin biyu a matsayin wata alama da ke nuni da kyakkyawan kudurin gwamnatin Malam Umar Namadi wajen samar da hanyoyin mota ga yankunan karkara, inda fiye da kaso 60 na jama’ar jihar ke zaune.

Bayan samun goyon baya da gagarumin rinjaye sai aka yiwa kudurorin 3 karatu na 2, daga nan kuma shugaban majalisar dokokin jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya mika kudurori 2 na hanyoyin mota a yankunan karkara ga kwamatin muhalli, yayin da kudurin kafa hukumar inganta kwazon malamai ya je ga kwamatin ilimi mai zurfi da na ilimi matakin farko, wanda dukkan su aka bai wa makonni 4 domin mika rahotannin su.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Bayelsa ya fice daga jam’iyyar PDP
  • Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
  • ’Yan bindiga sun kai hari a Kankia
  • Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato
  • Shugaban Hukumar Zaɓen Yobe Jihar Yobe ya rasu
  • Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba
  • Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA
  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano