Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya zargi tsohon shugaban kasar Barack Obama da cin amanar kasa tare da yin kira da a yi masa shari’a

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya zargi magabacinsa, Barack Obama da cin amanar kasa, inda ya bukaci a gurfanar da shi a gaban kuliya kan wani rahoton sirri da ya nuna cewa; Jami’an gwamnatin Obama sun murguda bayanai game da katsalandan din Rasha a zaben Amurka na shekara ta 2016.

Kalaman na Trump sun zo ne yayin wani taron manema labarai a ofishin Oval, wanda shugaban kasar Philippines Ferdinand Marcos ya halarta. Yana cewa:”Bisa ga abin da ya karanta…tsohon shugaba Obama ne ya fara wannan badakalar,” ya kara da cewa Obama shi ne “shugaba” na abin da ya bayyana a matsayin “gungun maciya amana.”

An karfafa wadannan zarge-zarge ne bayan da Daraktar hukumar leken asirin kasar Tulsi Gabbard ta aike da masu gabatar da kara ga ma’aikatar shari’a dangane da wani rahoto da aka fitar a ranar Juma’ar da ta gabata da ke tabbatar da cewa jami’an gwamnatin Obama na da hannu wajen kirkirar bayanan sirri da nufin share fagen juyin mulki na tsawon shekara daya kan shugaba Trump.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Shugaban kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

Babbar Kotun Tarayya da ke Bauchi ta yanke hukunci a kan gwamnatin jihar Bauchi da ta biya tsohon Akanta-Janar na jihar, Dakta Sa’idu Abubakar, Naira miliyan 100 a matsayin diyyar take masa haƙƙi da kuma tsare shi ba bisa ƙa’ida ba. Kotun ta kuma umarci gwamnati ta wallafa ban haƙuri a manyan jaridu guda biyu cikin kwanaki 14.

Mai Shari’a Aminu Garba ya yanke wannan hukunci ne a ƙarar da Dakta Abubakar ya shigar, yana zargin gwamnati da jami’anta da take masa haƙƙi, da kama shi ba tare da bin ƙa’ida ba, da musgunawa. Ya bayyana cewa hakan ya saɓawa tanade-tanaden kundin tsarin mulki da kuma yarjejeniyar kare haƙƙin bil’adama ta Afrika.

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi

Waɗanda kotun ta bayyana da laifi sun haɗa da shugaban ƴansanda na ƙasa, kwamishinan ƴansanda na Bauchi, gwamnatin jihar Bauchi, Antoni Janar na jihar da hukumar karɓar ƙorafe-ƙorafe ta jihar. Kotun ta tsame hukumar DSS daga cikin hukuncin, saboda babu isasshen hujja kan rawar da ta taka.

A ƙarshe, kotun ta hana duk wani ƙarin cin mutunci, tsarewa ko kama Dakta Abubakar ba tare da bin doka ba. Haka kuma ta jaddada cewa ya cancanci diyya saboda hana shi walwala da damuwa da aka jefa shi ciki daga ranar 9 zuwa 25 ga Disamba, 2024.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da  Falasdinu a matsayin Mamba
  • Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco