A binciko mesar da ta ɓace a Kano — Sanusi II
Published: 22nd, July 2025 GMT
Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yi kira ga kwamishinan ‘yan sanda Ibrahim Adamu Bakori, da ya tsaurara bincike domin gano mesar da ake zargi mallakin tsohon Akanta-Janar Ahmed Idris ce ta kuɓce kuma ta shiga gari.
Sarkin ya yi jan hankalin ne lokacin da al’ummar unguwar Daneji, bisa jagorancin mai unguwar Malam Abba Lawan suka kai masa koke, kan yadda tsohon Akantan ya ajiye dabbobi masu hadari a gidansa da sunan kiwo, har ake yanka musu shanu domin ciyar da su.
Sarkin ya kuma ja hankalin tsohon Akantan kan illar ajiye dabbobin a tsakiyar jama’a, tare da yin kira a gare shi da ya gaggauta dauke su, domin gudun abinda ka-je-ka-zo.
Idan za a iya tunawa dai Aminiya ta rawaito yadda ake zargin Akantan da kiwon namun dajin da suka hada da zakuna, da kada, da macizai da kuma mesa, har ma yake yanka musu shanu a bainar jama’a.
A tattaunawarmu da Mai Unguwar, Malam Abba, ya bayyana mana yadda ya jagoranci al’ummar har gaban Sarki, domin neman dauki.
“Lamarin ya faru kafin ranar Juma’a, amma ba mu samu tabbas ba har sai ranar Juma’ar. Na je na same shi da kaina na yi masa magana, na kuma fada masa illar ajiye dabbobi masu hadari a tsakiyar al’umma ya kuma yi min alkawarin zai kwashe.
“Da fari ma da cewa ya yi ba yanzu zai kwashe ba, sai na ce masa sai sun yi girman da za su hadiye wani tukunna? Sai ya ce “za a dauke”.
“Da na ga bai kwashe ba, sai na rubuta rahoto na aika wa Wakilin Kudu, shi kuma ya aika wa Wakilin Hakimi, har zuwa gaban Sarki.
“A yau kuma mun je gaban Sarki mun sanar da shi halin da ake ciki. Kuma an karanta masa takardarmu, ya kuma bayar da umarnin mu je a rubuta wa kwamishinan ‘yan sanda a hukumance, domin su ne suke da hakkin binciken abinda yake gudana.
“Muna sa ran gobe Talata za a kai takardar in sha Allah,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sarkin Kano Tsohon Akanta Janar
এছাড়াও পড়ুন:
Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano
Mazauna unguwar Zangon Kaya da ke karamar hukumar Dawakin Tofa a jihar Kano sun shiga cikin makoki sakamakon nutsewar da wasu matasa hudu suka yi a hanyar ruwa da baraguzan gine-gine suka tushe.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Yusif, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin.
A cewarsa, lamarin ya faru ne bayan wadanda lamarin ya rutsa da su suka shiga mashigar ruwa da suka taru sakamakon toshewar hanyar jirgin da ake yi.
Ya kara da cewa, kamar yadda shaidun gani da ido suka bayyana, da farko biyu daga cikin wadanda abin ya shafa sun shiga cikin ruwan da nufin yin iyo amma sun makale. A kokarin ceto su, mutum na uku ya shiga, shi ma ya makale. Abin baƙin ciki, mutum na huɗu, yana ƙoƙari ya ceci sauran, ya fuskanci irin wannan matsalar.
Saminu ya yi nuni da cewa, kafin isowar hukumar kashe gobara mazauna yankin sun yi nasarar ceto biyu daga cikin wadanda abin ya shafa. Yayinda “Sauran biyun, tawagar ceto ta fito da
Wadanda abin ya shafa sun hada da Nasirudden Tasi’u dan shekara 25 da Basir Sani mai shekaru 28 da Yakubu Muhd dan shekara 22 da Usman Ubale dan shekara 26.
Jami’in hulda da jama’a ya yi nuni da cewa, an samu dukkanin mutane hudun a sume kuma daga baya aka tabbatar da sun mutu.
“An mika gawar su ga SP Abdulkadir M. Albasu na sashin ‘yan sanda na Dawanau domin ci gaba da bincike”.
Saminu ya ce, Daraktan hukumar kashe gobara ta jiha Alhaji Sani Anas ya jajantawa iyalan mamatan.
Ya kuma gargadi jama’a da su guji shiga cikin ruwa ba tare da izini ba ko kuma masu hadari, musamman wadanda ayyukan gine-gine ya shafa.
“Muna kira ga ‘yan ƙasa da su guji yin iyo ko wasa a cikin kududdufi, musamman waɗanda aka toshe ko ba a tsara su don amfani da nishaɗi ba.
Al’umma na ci gaba da nuna alhininsu yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike kan al’amuran da suka dabaibaye wannan mummunan lamari.
Rel/Khadijah Aliyu