Aminiya:
2025-11-03@03:53:41 GMT

A binciko mesar da ta ɓace a Kano — Sanusi II

Published: 22nd, July 2025 GMT

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yi kira ga kwamishinan ‘yan sanda Ibrahim Adamu Bakori, da ya tsaurara bincike domin gano mesar da ake zargi mallakin tsohon Akanta-Janar Ahmed Idris ce ta kuɓce kuma ta shiga gari.

Sarkin ya yi jan hankalin ne lokacin da al’ummar unguwar Daneji, bisa jagorancin mai unguwar Malam Abba Lawan suka kai masa koke, kan yadda tsohon Akantan ya ajiye dabbobi masu hadari a gidansa da sunan kiwo, har ake yanka musu shanu domin ciyar da su.

A tsananta hukunci kan masu dukan mata — Sarki Sanusi Yunwa na ƙara tsanani a Arewa maso Gabashin Nijeriya — ICRC

Sarkin ya kuma ja hankalin tsohon Akantan kan illar ajiye dabbobin a tsakiyar jama’a, tare da yin kira a gare shi da ya gaggauta dauke su, domin gudun abinda ka-je-ka-zo.

Idan za a iya tunawa dai Aminiya ta rawaito yadda ake zargin Akantan da kiwon namun dajin da suka hada da zakuna, da kada, da macizai da kuma mesa, har ma yake yanka musu shanu a bainar jama’a.

A tattaunawarmu da Mai Unguwar, Malam Abba, ya bayyana mana yadda ya jagoranci al’ummar har gaban Sarki, domin neman dauki.

“Lamarin ya faru kafin ranar Juma’a, amma ba mu samu tabbas ba har sai ranar Juma’ar. Na je na same shi da kaina na yi masa magana, na kuma fada masa illar ajiye dabbobi masu hadari a tsakiyar al’umma ya kuma yi min alkawarin zai kwashe.

“Da fari ma da cewa ya yi ba yanzu zai kwashe ba, sai na ce masa sai sun yi girman da za su hadiye wani tukunna? Sai ya ce “za a dauke”.

“Da na ga bai kwashe ba, sai na rubuta rahoto na aika wa Wakilin Kudu, shi kuma ya aika wa Wakilin Hakimi, har zuwa gaban Sarki.

“A yau kuma mun je gaban Sarki mun sanar da shi halin da ake ciki. Kuma an karanta masa takardarmu, ya kuma bayar da umarnin mu je a rubuta wa kwamishinan ‘yan sanda a hukumance, domin su ne suke da hakkin binciken abinda yake gudana.

“Muna sa ran gobe Talata za a kai takardar in sha Allah,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sarkin Kano Tsohon Akanta Janar

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta tsige dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi daga kujerarsa saboda sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.

Gummi yana wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara a majalisar wakilai.

An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku

Mai shari’a Obiora Egwuatu ne, ya yanke hukuncin, inda ya umarci kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, da ya daina amincewa da Gummi a matsayin dan majalisar da ke wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum.

Haka kuma ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta shirya sabon zabe cikin kwanaki 30 domin cike gurbin kujerar dan majalisar.

Jam’iyyar PDP tare da shugaban ta na jihar Zamfara, Jamilu Jibomagayaki, ne suka shigar da karar dan majalisar.

Sun ce bai dace Gummi ya ci gaba da zama a kujerar ba bayan barin jam’iyyar da ta tsayar da shi takara.

Gummi, ta bakin lauyansa ya ce ya fice daga PDP ne saboda rikicin cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi a matakin kasa da kuma a mazabarsa.

Amma kotu ta yi watsi da wannan hujjar, inda ta bayyana cewa babu takaddama da za ta ba shi damar ya sauya sheka.

A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Egwuatu ya ce ’yan siyasa dole su mutunta zabin jama’ar da suka kada musu kuri’a a karkashin jam’iyyar da ta tsayar da su takara.

Ya ce doka ba ta yadda da dan siyasa ya bar jam’iyyar da ta taimaka masa wajen lashe zabe sannan ya koma wata jam’iyya ba tare da ajiye mukaminsa ba.

Ya kara da cewa kuri’un da aka kada don dan takarar na jam’iyya ne, ba nasa ne na kashin kansa ba.

“Idan mutum yana son sauya sheka, ka da ya dauki amanar jama’ar da ta zabe shi ya tafi da ita,”  in ji alkalin.

Kotu ta kuma umarci Gummi da ya daina karbar albashi da wasu hakkoki a matsayin dan majalisa, tare da mayar da duk kudaden da ya karba daga ranar 30 ga watan Oktoba, 2024, zuwa ranar da aka yanke hukuncin.

Haka kuma, ya gabatar da hujjar mayar da kudaden ga kotu cikin kwanaki 30.

Mai shari’a Egwuatu ya kuma ci Gummi tarar Naira N500,000, domin biyan PDP kudaden da ta kashe wajen shigar da kara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Maganin Nankarwa (3)
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure