Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Published: 12th, July 2025 GMT
Rahotanin sun bayyana cewa Shettima ya ziyarci Kano ne don yin ta’aziyyar rasuwar hamshakin dan kasuwa, Alhaji Aminu Dantata, wanda ya rasu kwanan nan, da kuma jajanta wa mutanen Kano kan wannan rashi.
Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa a irin wadannan manyan taruka a Nijeriya, an saba ganin shugabannin jam’iyya da goyon baya su tarbi manyan jami’ai kamar mataimakin shugaban kasa, amma lamarin ya bambanta yayin ziyarar Shettima, wanda ya haifar da zazzafar muhawara.
Da yake musanta cewa akwai rikice-rikice na cikin gida a jam’iyyar, sakataren APC a Kano, Ibrahim Zakari Sarina, ya shaida cewa rashin halartar shugabannin jam’iyyar a ziyarar ta’aziyya da mataimakin shugaban kasa ya kawo Kano ya faru ne sakamakon rashin sadarwa.
“Mun san cewa ziyarar za ta kasance, amma sadarwa ta zo a makare. Kafin mu shirya, mun riga mun makara. Saboda gwamnatin ta riga ta shirya tun kafin mu isa wurin.
“A gaskiya wannan abu ba ya da alaka da kowanne irin lamari na siyasa. An sanar da mu a makare, har ita kanta gwamnatin jihar a makare aka sanar da ita. Daga baya mun aike da godyarmu ga mataimakin shugaban kasa bisa ziyara, kuma ya fahimci yanayin sosai,” in ji Sarina.
Duk da wannan bayani, an samu rarrabuwan kai a tsakanin ‘yan siyasa a jihar.
Wani jigo a APC a yankin Gwale, Abdullahi Kabiru, ya bayyana cewa ya ji takaicin rashin halartar shugabannin jam’iyyar. “Wannan shi ne mataimakin shugaban kasa na wannan kasa, kuma ba mu kasa shirya tarba a gare shi ba? Wannan ba karamin kuskure ba ne. Ko da an samu rashin kyakkyawan sadarwa, yana nuna cewa akwai rashin hadin kai,” in ji shi.
Ita kuwa wata mai kishin jam’iyya, Amina Sani daga Tarauni, ra’ayinta ya sha bamban. Ta ce, “Na gamsu da bayanin da jam’iyyar ta bayar. Abubuwa suna faruwa a siyasa, musamman lokacin da jadawalin ke canzawa. Amma ina fatan hakan ba zai zama sabani ba. Dole ne mu girmama shugabanninmu da ofisoshinsu ba tare da la’akari da kowanne bambancin siyasa ba.”
Da yake jawabi kan lamarnin, wani masana harkokin siyasa, Dakta Musa Auwal ya bayyana cewa dole ne jam’iyyar ta yi taka-tsantsan. “Ko lamarin ya faru da gangan ko akasin haka, a duk lokacin da aka samu rarrabukan na manyan shugabannin jam’iyya a fili, yana rage karfin jam’iyyar kuma yana karfafa ‘yan adawa.
“APC a Kano tana taka muhimmiyar rawa a siyasan kasar nan, kuma kowanne takaddama da ke tasowa Kano na shugabancin ko na siyasa na iya zama babban lamari da ke daukan tsawon lokaci ana tattaunawa a kai,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi
An dai yi ta tsokaci kan cewa ko Obi zai amince da mukamin mataimakin shugaban kasa tare da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, kamar yadda ya yi a 2019.
Obi ya ce, “Takarar shugaban kasan Nijeriya zan yi a 2027, kuma na tabbatar da cancanta.”
A kan ko zai hakura ya zama mataimakin takarar Atiku a 2027, Obi ya bayyana cewa, “Wannan abun wasa ba ne, babu wanta ya tattauna hakan. Mutane ne kawai yin irin wannan tunani. Amma a zahirin gaskiya babu wanda ya bayyana hakan.”
Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya kuma jaddada cewa har yanzu yana shi mamba ne a jam’iyyar LP.
LEADERSHIP ta ruwaito cewa Obi yana daga cikin shahararrun mutane a cikin hadakar ADC da ‘yan adawar masu kokarin karbe mulki a wurin Shugaban kasa Bola Tinubu na jam’iyyar APC, wanda ke neman zarcewa a wa’adi na biyu a zaben 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp