Aminiya:
2025-07-23@17:27:05 GMT

DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Published: 23rd, July 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A duk lokacin da aka ce an kammala zangon karatu, dalibai kan samu hutu don hutawa da yin wadansu abubuwa na daban da kuma ba su damar shakuwa da ’yan uwa da abokan arziki.

Kamar yadda masana harkar harkar ilimi suka saba fadi, yawan karatu kan taho da nashi irin matsalolin, ya kuma kamata a ce ana ware wa dalibai wasu lokuta na musamman don samun hutu daga karatun da suka koya.

NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa DAGA LARABA: Makomar Siyasar Najeriya Bayan Rasuwar Shugaba Buhari

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan abubuwan da ya kamata yara su ringa yi yayin hutun makaranta.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hutun Makaranta Zangon Karatu

এছাড়াও পড়ুন:

Manoma A Kaduna Sun Yabawa Irin Masara Na TELA Saboda Juriyarshi Ga Kwari

 

Manoma a Jihar Kaduna sun bayyana gamsuwarsu da yadda iri na TELA Hybrid Maize daga kamfanin EcoBasic Seeds ke samar da amfanin gona ba tare da amfani da maganin kwari ba.

 

Sun bayyana hakan ne a Jaji, Jihar Kaduna, lokacin da ‘yan jarida suka kai ziyara gonakin gwaji da kamfanin EcoBasic Seeds ya kafa.

 

Wani daga cikin manoman, Mallam Sabitu Abdullahi, ya bayyana Irin Masara na TELA Hybrid a matsayin masara mai ban mamaki, yana cewa tana bada amfanin gona mai yawa da kuma girbi cikin kwanaki 70 kacal.

 

“Idan duka manoman Najeriya suka rungumi wannan iri, zai taimaka wajen tabbatar da wadatar abinci a kasa,” inji shi.

 

Ya ce ya shafe shekaru uku yana amfani da irin Masara TELA a gonakin gwaji, kuma ba su yi nadama ba.

 

“Ina noma don cin abinci ne da siyarwa. Mun yi tuwo da ita kuma lafiyayya ce,” ya kara da cewa.

 

Sabitu ya bayyana cewa ya dasa irin SAMMAZ 75 T a gonarsa, wanda kuma za a iya sake dasa shi. Ya shawarci sauran manoma su rungumi irin Masara na TELA, tare da bukatar su sayi iri tun kafin damina mai zuwa.

 

Ya koka da cewa kafin zuwan irin Masara na TELA, manoma a Najeriya na fama da asarar amfanin gona saboda fari, kwari irinsu stemborer da sauran su, amma yanzu sun fara cin gajiyar karin amfanin da ya kai kashi 30 cikin 100.

 

Haka zalika, matarsa, Aminat Sabitu, wata manomiya, ta ce ta shiga harkar noma tare da mijinta bayan ganin irin yawan amfanin da irin Masara na TELA Maize ke bayarwa.

 

“Tun da muka fara amfani da irin Masara na TELA, muna samun buhuna 22 daga filin da muke samun buhuna 10,” inji ta, tana mai cewa irin na da juriya ga fari kuma yana karɓar taki sosai.

 

Ta bukaci kungiyoyin mata su fito su fara shuka irin Masara na TELA, tana tabbatar musu ba za su yi nadama ba.

 

Isma’il Shaibu, matashi mai shekara 27 da haihuwa, ya bayyana cewa irin Masara na TELA Maize ita ce masarar da ta fi dacewa.

 

“Da can ina samun buhuna 7, amma yanzu ina samun 13 daga fili ɗaya. Ba sai mun feshi da maganin kwari ba, saboda wannan iri yana da juriya,” inji shi.

 

Ya kara da cewa kafin su gwada TELA suna da ra’ayi mara kyau a kanta, amma tun da suka fara amfani da ita, suka cigaba da nomanta.

 

A wani bangare, Saleh Ahmadu da aka hangosu yana shara a gonarsa, ya ce ya shafe fiye da shekaru 20 yana noma amma bai taba ganin irin TELA Maize ba.

 

“Kwari ba su cika cin ganyenta ba, kuma tana bada yawan amfanin gona. Idan wani iri zai baka buhuna 5, wannan zai baka sau biyu daga fili ɗaya,” ya bayyana.

 

Cov: Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Amince Da Nadin Sabbin Sakatarori Guda Takwas
  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
  • Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati
  •  Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta
  • UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara
  • NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa
  • Jihohin da za a samu ruwan sama da iska mai ƙarfi a sassan Nijeriya — NiMet
  • Manoma A Kaduna Sun Yabawa Irin Masara Na TELA Saboda Juriyarshi Ga Kwari
  • Gwamna Radda Da Makarrabansa Na Samun Kulawa A Asibiti Bayan Hatsarin Mota A Hanyar Daura