Ministan yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila yana alfahari da rusa Gaza da tarwatsa mazauna yankin!

Isra’ila Katz, ministan yakin gwamnatin mamayar Isra’ila, ya wallafa wani hoto da ya nuna yadda aka lalata garin Beit Hanoun a arewacin zirin Gaza, yana mai alfahari da yadda aka rusa gine-ginen garin”.

Kuma ta hanyar dandalin “X”, Kats yayi sharhi game da hoton, yana cewa: “Bayan Rafah da Beit Hanoun.. babu mafaka ga ‘yan ta’adda.

Hoton da aka dauka ta sama yana nuni da dimbin baraguzan gine-gine da kango da kuma irin barnar da aka yi wa daukacin garin da ke daura da layin da aka shimfida da tarwatsewar kango da ragowar gine-ginen da suka ruguje a hoton inda ke nuni irin girman bala’in da ya afku a yankin.

Beit Hanoun shi ne yanki na farko da sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila suka mamaye a farkon harin na kasa a Gaza a ranar 28 ga watan Oktoban shekara ta 2023, a ci gaba da yakin kisan kiyashi bayan barna da Falasdinawan sama da dubu 195 suka yi shahada da kuma jikkata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Iran ba za ta iya watsi da shirinta na inganta sinadarin Uranium ba

Ministan harkokin wajen na Iran ya fada a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Fox News cewa: Har yanzu ba a dakatar da inganta sinadarin Uranium ba a Iran, duk da irin barnar da aka mata bayan hare-haren da Amurka ta yi mata mai tsanani.

A cikin wata hira da gidan talabijin na Fox News, Araqchi ya ce, “Shin shirin inganta sinadarin Uranium a Iran ya dawo? Shin har yanzu wannan shirin yana ci gaba, ko kuwa barnar da aka yi ta yi tsanani har ta kai ga dakatar da shi gaba daya?” Ya ce: “Ba a dakatar da shi ba, duk da cewa barnar ta yi muni da yawa, amma ba shakka ba za a iya yin watsi da Shirin inganta sinadarin Uranium ba, domin wannan nasara ce ta masana kimiyyar Iran, kuma a halin yanzu abin alfahari ne ga kasar, kuma inganta sinadarin Uranium yana da matukar muhimmanci a gare ta.”

Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa: “Iran ba zata taba matsawa wajen inganta sinadarin uranium da kashi 90 cikin dari ba. Iran ta himmatu wajen tabbatar da samar da makamashin Uranium kasa da kashi 5% domin samar da makamashin nukiliya. Kuma tana inganta sinadarin na Uranium zuwa kashi 20% saboda tana da injin binciken TRR.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta
  •  Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba
  • Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
  • Manoma A Kaduna Sun Yabawa Irin Masara Na TELA Saboda Juriyarshi Ga Kwari
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza
  • MDD Ta Gargaɗi Isra’ila Kan Tilasta Wa Al’ummar Deir al-Balah Na Gaza Tashi
  • Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; Iran Ba Zata Bar Tace Sinadarin Uranium Ba
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi