Aminiya:
2025-07-12@17:05:58 GMT

Jami’ar Yobe sun tsunduma yajin aiki

Published: 12th, July 2025 GMT

Ƙungiyar Malaman Jami’a ta Ƙasa (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Yobe (YSU), ta fara yajin aikin sai baba-ta-gani saboda gwamnati ta kasa cika alƙawuran da ta ɗaukar musu.

Waɗannan alƙawura sun haɗa da ƙarin albashi, biyan bashin da suke bi, da kuma barin jami’ar ta riƙa gudanar da harkokinta da ƙashin kanta.

Lakurawa sun kashe ’yan sanda 3 a Kebbi Yadda aka kama ɗan bindiga ɗauke da N13m a hanyar Jos

Shugaban ASUU na Jami’ar Yobe, Dokta Ahmed Karage, ya bayyana hakan bayan kammala wani taro da suka gudanar.

Ya ce sun fara yajin aikin ne bayan dogon lokaci da suka ɗauka suna tattaunawa da gwamnati, amma ba su cimma matsaya ba.

“Mun kwashe watanni muna magana da gwamnati, amma abin takaici shi ne dole ne yanzu mu tafi yajin aiki saboda gwamnati ta ƙi cika alƙawuran da ta ɗauka,” in ji Dokta Karage.

Daga cikin buƙatunsu akwai aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000, biyan bashin albashin da ya fara tun daga shekarar 2019, da kuma wasu haƙƙoƙinsu.

Ya ce jami’o’i su riƙa tafiyar da al’amuran su da kansu shi ne mafita don warware matsalolin da ake fama da su a fannin ilimi.

ASUU ta ce ba za su koma aiki ba har sai gwamnati ta magance matsalolin da suka gabatar.

Sun gargaɗi gwamnatin jihar kan ɗaukar matakin gaggawa don kaucewa kawo cikas ga kalandar karatu.

Har ila yau, ƙungiyar ta roƙi dalibai da su yi haƙuri, inda ta ce ta fara yajin aikin ba don cutar da su ba, illa dai domin neman haƙƙinsu da ya wajaba gwamnati ta biya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Jami ar Yobe Ƙarin Albashi Yajin aiki gwamnati ta da gwamnati

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista

Ya ƙara da cewa, Tinubu na mutunta dimokuraɗiyya da doka.

Haka kuma, gwamnati ta san cewa ba za ta iya aiki yadda ya kamata ba tare da kafafen yaɗa labarai ba.

Idris ya ce a baya, wasu jami’an gwamnati suna sukar gwamnati, amma shi kullum yana tattaunawa da ƙungiyar ’yan jarida da masu wallafa jaridu domin warware matsaloli cikin lumana.

“Idan muna yin daidai, ku yabe mu,” in ji shi.

“Idan kuma muna kuskure, ku faɗa mana cikin lumana domin mu inganta ayyukanmu.”

Ministan ya ce gwamnatin Tinubu tana da kyakkyawar mu’amala da kafafen labarai kuma hakan zai ci gaba.

Ya roƙi ’yan jarida ka da su ɗauki wasu ƙananan matsaloli su yi wa gwamnati hukunci a kai gaba ɗaya.

Ya kuma bayyana wani babban ci gaba da aka samu a Nijeriya na dab da samuwa domin za a karɓi baƙuncin Cibiyar Wayar da Kan Jama’a kan Hanyoyin Yaɗa Labarai (MIL) a Jami’ar Open University da haɗin gwiwar UNESCO.

Wannan cibiyar za ta taimaka wajen ilimantar da mutane kan labaran ƙarya da yaɗa jita-jita.

“Da zarar an amince, mutane daga sassa daban-daban na duniya za su riƙa zuwa Nijeriya domin koyon dabarun kafafen yaɗa labarai,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’ar Yobe ta tsunduma yajin aiki
  • Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi
  • Malaman Jihar Jigawa Sun Karrama Shugaban Hukumar Alhazai Ta Jihar
  • Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote
  •  Masu Kare Hakkin Dan’adam Suna Allawadai Da Takunkumin Amurka  Akann Jami’ar MDD A Falasdinu
  • Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawa
  • Tinubu Bai Taɓa Ba Ni Umarnin Yin Ƙarya Ko Cin Zarafin ’Yan Jarida Ba – Minista
  • An Fara Taron Nishan Karo Na 11 Game Da Wayewar Kai A Duniya
  • Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 30 a Katsina