Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; An Mika Batun Hakin Gwiwa Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA Ga Kwamitin Kolin Tsaron Kasa
Published: 12th, July 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: An mika fayil ɗin haɗin gwiwa tare da Hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ga kwamitin koli na tsaron ƙasa
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana a wata ganawa da jakadun kasashen waje da na kasa da kasa cewa: Iran bangare ce a yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta “NPT” kuma tana yin aiki da tanade-tanaden da aka yi mata, amma idan aka yi la’akari da sabbin yanayi da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, hadin gwiwarta da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA za ta dauki wani sabon salo.
Yayin da yake ishara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana ci gaba da tsayawa tsayin daka kan yarjejeniyar tsaron da aka kulla tsakaninta da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya, Araqchi ya ce: Hadin gwiwar Iran da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya bai tsaya ba, amma idan aka yi la’akari da sabbin yanayi da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, wannan hadin gwiwa zai dauki wani sabon salo. Wannan gaba ɗaya al’ada ce kuma ana tsammanin hakan.
Shugaban jami’an diflomasiyyar na Iran ya ci gaba da cewa: Kamar yadda dokar majalisar shawarar Musulunci ta tanada, daga yanzu, kwamitin koli na tsaron kasar zai gudanar da dukkanin hadin gwiwar da Iran za ta yi da hukumar ne kawai, kuma wannan majalisar za ta yi nazari tare da yanke hukunci kan kowane lamari da hukumar ta bukaci ci gaba da sanya ido a Iran. Za a gudanar da waɗannan bita tare da cikakken la’akari da lura cikin aminci da tsaro.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: da hukumar kula da makamashin nukiliya ta
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
Manajar ofishin na NIWA, da ke a jihar ta Legas Injiniya Sarat Braimah ta bayyana cewa, tura ma’ikatan hukumar domin yin aikin, zai taimaka wajen gudanar da aikin a cikin inganci.
Kazalika, ya sanar da cewa, hakan zai kuma bayar da damar yin safarar kaya a cikin sauki da kuma safarar matafiya da ke bin hanyar ruwa ta yankin na Ikorodu.
“Mun yi nazari a cikin kwanciyar hankali kan yadda za a tabbatar da an cire fulawar da ke a cikin kasan ruwan ba tare da wata miskila ba tare da kuma bai wa jiragen ruwan damar yin zirga-zirgarsu a hanyoyin ruwan, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Injiya Braimah.
“ Aikin ya wuce batun fannin samar da saukin yin sufurin jiragen ruwan har da tabbatar da an kiyaye janyo matsala ga ayyukan kamun Kifi a hanyoyin na ruwan, “ A cewar Inji Manajar.
Ta kara da cewa, babban shugabanmu na hukumar ta NIWA, Bola Oyebamiji, ne tuni ya riga ya bayar da kwangilar yin aikin, ba wai a jihar Legas kawai ba, har da a sauran hanyoyin ruwa da ke a sassan kasar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA