Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar
Published: 22nd, July 2025 GMT
Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya, Hajiya Amina Mohammed, ta yaba wa Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bisa kokarinsa wajen inganta ci gaban zamantakewar al’umma da kuma tallafawa aiwatar da Muradun Cigaba mai Dorewa (SDGs).
Hajiya Amina Mohammed ta kai ziyara Jihar Kano ne domin yin ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar jihar bisa rasuwar fitattun dattawan nan biyu, wato Alhaji Aminu Alhassan Dantata da tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.
A yayin ziyarar tata, Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniyar ta nuna gamsuwa da wasu daga cikin shirye-shiryen Gwamna Yusuf na cigaban al’umma, musamman wadanda suka yi daidai da muradun ci gaban duniya.
Daga cikin wadannan shirye-shirye akwai sanya fitilu masu amfani da hasken rana a titunan Kano, kafa cibiyar kula da cututtuka ta Kano (Kano Centre for Disease Control), wadda ita ce irinta ta farko da wata gwamnati ta jiha ta kafa a Najeriya, da kuma kokarin fadada tsarin inshorar lafiya domin al’ummar jihar su amfana.
Ta kuma yaba da kirkirar Ma’aikatar Wutar Lantarki da Makamashi, tare da sake tsara Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi, wanda dukkansu ke nuni da jajircewar gwamnati wajen daukar matakan kare muhalli da dorewar ci gaba.
Hajiya Mohammed ta bayyana cewa ziyarar tata ba wai kawai domin ta’aziyya ba ce, har da zurfafa wayar da kai kan Muradun Ci Gaba Mai Dorewa, da kuma karfafa hadin gwiwa da jihar Kano.
Ta sanar da gwamnan game da babban taron Kasuwanci da Zuba Jari na Majalisar Dinkin Duniya da ke tafe, tare da nuna godiya bisa dagewarsa wajen karfafa mata, samar da ayyukan yi, da kare muhalli.
A nasa jawabin , Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa a shirye jiharsa take ta hada gwiwa da Majalisar Dinkin Duniya musamman a fannonin ilimi, lafiya, sauyin yanayi, samar da makamashi, kare muhalli da kuma zuba jari mai dorewa.
Ya jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da aiwatar da manufofin ci gaba da za su inganta rayuwar al’ummar Kano da kuma bada gudunmawa ga kokarin ci gaban duniya.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Majalisar Dinkin Duniya
এছাড়াও পড়ুন:
Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila
Jaridar Washington Post ta bayyana cewa: Cikakken gurgunta tashar jiragen ruwa na Eilat da ke haramtacciyar kasar Isra’ila ya bayyana tasirin ikon Yemen
Jaridar Washington Post ta Amurka ta tabbatar da cewa rufe tashar jiragen ruwa ta Umm al-Rashrash na karshe ya nuna tasiri da karfin hare-haren Yemen ke da shi.
A cikin wani babban rahoto da aka buga a ranar Litinin, jaridar ta lura cewa, bayanan da jami’an mamayar Isra’ila suka yi game da gurguncewar da tashar jiragen ruwa ta yi, sun bayyana a fili “cikakkiyar nasarar da ‘yan Yemen suka yi.”
Jaridar ta yi hasashen cewa: Kasar Yemen za ta iya aiwatar da sauye-sauyen dabarun yaki a yankin, inda ta yi nazari kan wasu ayyukan sojojin ruwan kasar Yemen da suka tilastawa jiragen yakin Amurka gudu daga yankin, tare da sanadin nutsewar jiragen ruwa da dama da suka sabawa umarninsu, lamarin da ya sa sojojin Amurka da na yammacin Turai suka kasa yin komai a kansu.
Jaridar ta lura cewa ayyukan Yemen sun sanya tasirin su tun farkon harin da suka kai ga jirgin ruwan jigilar gwamnatin mamayar Isra’ila a karshen shekara ta 2023, da ya tabbatar da cewa ayyukan sun ragu da kashi 90 cikin 100 cikin kankanin lokaci, kafin tashar ta kai ga barin aiki kwata-kwata.