Gwamnatin Mauritaniya Ta Karyata Rahoton Cewa Shugaban Kasarta Ya Gana Da Netanyahu
Published: 12th, July 2025 GMT
Gwamantin kasar Mauritaniya ta musanta cewa shugabanta ya gana da Netanyahu, ta yi kira ga tashar Al Arabiya da ta tabbatar da sahihancin rahoton kafin watsa shi
Ministan al’adu da sadarwa na Mauritaniya kuma mai magana da yawun gwamnatin kasar Hussein Ould Maddou ya musanta sahihancin rahotannin ganawar da ake zargin shugaban kasar Mauritaniya da Fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu.
Kamfanin dillancin labaran Jamus ya nakalto ministan na cewa rahoton da tashar Al Arabiya ta watsa game da ganawar da ake zargin shugaba Mohamed Ould Ghazouani da Fira ministan Igwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ba shi da tushe balle makama.
Ya yi nuni da cewa, labaran ba su da inganci, inda ya yi kira ga tashar Al-Arabiya da ta kasance mai gaskiya wajen samun bayanai tare da kaucewa yada labaran karya.
Kakakin gwamnatin ya kuma jaddada cewa: Daya daga cikin muhimman ayyuka na sana’ar jarida shi ne dogaro da majiyoyin hukuma, musamman idan aka yi la’akari da budi da saukin da ake baiwa wadannan majiyoyi manyan a tsakanin kafafen yada labarai masu neman sahihan bayanai.
Shugaban Mauritaniya ya halarci taron hadin gwiwa tsakanin shugaban Amurka Donald Trump da wasu shugabannin Afirka biyar kan hadin gwiwar tattalin arziki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar
Yau Lahadi al’ummar Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar.
Masu kada kuri’a miliyan takwas ne aka tantance domin kada kuri’a a zaben zagaye na farko da Shugaban kasar mai ci Paul Biya mai shekara 92 dake neman wa’adi na takwas.
A cikin makonni biyu na yakin neman zaben, Shugaba Biya wanda aka dade ba a gan shi a bayyanar jama’a ba ya gudanar da gangami guda daya kacal, a garin Maroua dake yankin Arewa mai Nisa, daya daga cikin yankuna uku na arewa, inda ya sha alwashin magance matsalar tsaro da rashin aikin yi.
A hukumance dai ‘yan takara goma sha biyu ne ke fafatawa a wannan zaben, amma biyu sun janye.
Manyan masu kalubalantar Paul Biya guda biyu a wannan zaben su ne, Issa Tchiroma Bakary, na jam’iyyar CNSF, da Bello Bouba Maïgari, wanda zai iya dogaro da jam’iyyarsa ta (UNDP).
Batun tattalin arziki da rashin aikin yi da matsalar tsaro su ne suka fi mamaye yakin neman zaben.
Mista Biya na Jam’iyyar (RDPC), ya fara mulkin kasar ne tun shekarar 1982.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice October 12, 2025 Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine October 12, 2025 Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara October 12, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon October 12, 2025 An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Aka Tattauna Batun Falasdinu October 12, 2025 Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh October 12, 2025 China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100% October 12, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter A Kasar Habasha October 12, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan October 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci