Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna
Published: 11th, July 2025 GMT
“An tsara kungiyar ne domin hada kan Arewa da magance matsalar rashin aikin yi Wanda hakan ya sanya aka tattaro manyan hafsoshin soja da suka yi ritaya, da tsaffin gwamnoni, da masu rike da sarautun gargajiya, da masu fafutukar kare hakkin jama’a, da kungiyoyin matasa, da kwararrun a fannin ci gaban kasa wadanda da yawa daga cikinsu sun nuna rashin gamsuwa da yadda ake gudanar da mulki da kuma mayar da muradun Arewa saniyar ware a ‘yan shekarun nan”
“Yankin arewa na iya shawo kan kalubalen da suke fuskanta ta hanyar hadin kai da kuma sabunta kudurin samar da ci gaba,”
Bafarawa ya kuma tabbatar da cewa ba an kafa kungiyar bace a matsayin dandalin siyasa ba, kuma ba ta da shirin rikidewa zuwa jam’iyyar siyasa ba Yana Mai cewa kungiyace ta kawo hadin Kai da ci gaban yankin Arewa.
“Ba mu fito don yakar kowa ba amma don gina tubali da samar da kyakkyawar alaka Wanda kuma Manufarmu ta wuce siyasar bangaranci,” in ji shi.
Bafarawa ya kara da cewa, “Muna son duniya ta ga wani sabon labari da ya kunno kai daga yankinmu, wanda ke ba da kwarin gwiwa da juriya, da sauyi, wanda ke zai nuna cewa Eh, zaman lafiya mai yiwuwa ne da hadin a yankin Arewa”
Tsohon gwamnan ya bayyana mummunan halin da yankin Arewa ke ciki a halin yanzu, inda ya bayyana rashin tsaro da ake fama da shi, da rashin aikin yi ga matasa, da tabarbarewar dabi’u, da kuma talauci Inda yace abin takaici matuka.
Ya ci gaba da cewa kaddamar da kungiyar a daidai wannan lokaci Yana da matukar mahimmanci Domin fuskantar kalubalen da yankin Arewa yake fuskanta.
“kungiyar zata taimaka wajen Samar da Zaman lafiya da daidaito da kuma tattaunawa, hanyoyin da za’a Samar sa ci gaban Arewa ta bangarori daban-daban” in ji Bafarawa
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yankin Arewa
এছাড়াও পড়ুন:
Trump, da Al’Sisi za su jagoranci taron zaman lafiya kan Gaza a Masar ranar Litinin
Masar za ta shirya wani taron kasa da kasa kan zaman lafiya a birnin Sharm el-Sheikh da ke bakin Tekun Maliya a ranar Litinin, wanda Shugaba Abdel Fattah el-Sisi da takwaransa na Amurka, Donald Trump, za su jagoranta.
Wata sanarwa daga fadar shugaban kasar ta bayyana cewa taron zai tattaro shugabanni daga kasashe fiye da 20.
Manufar taron ita ce “kawo karshen yakin Gaza, da karfafa zaman lafiya da kwanciyar hankali a Gabas ta Tsakiya, da kuma fara wani sabon mataki na tsaro da kwanciyar hankali a yankin,” in ji sanarwar.
A ranar Laraba Trump ya sanar da cewa Isra’ila da Hamas sun amince da mataki na farko na wani shiri mai matakai 20 da ya gabatar a ranar 29 ga Satumba don cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza da sakin dukkan fursunonin Isra’ila da ke hannun Hamas a musayar fursunoni Falasdinawa kusan 2,000, da kuma janye sojojin Isra’ila daga dukkan yankin Gaza.
Mataki na biyu na shirin ya tanadi kafa sabon tsarin mulki a Gaza, samar da wata rundunar tsaro da za ta kunshi Falasdinawa da sojoji daga kasashen Larabawa da Musulmi, da kuma kwace makamai daga hannun Hamas.
Tun daga watan Oktoba na 2023, hare-haren Isra’ila sun kashe Falasdinawa fiye da 67,600 a Gaza, yawancinsu mata da yara, tare da mayar da yankin kufai.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka ‘Yan Kamaru na kada kuri’a a zaben shugaban kasar October 12, 2025 Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice October 12, 2025 Gwamnatin Cuba ta yi watsi da zargin da Amurka ke yi na hannu a yakin Ukraine October 12, 2025 Arachi: HKI Ba Abar Amincewa Ba Ce, Falasdinawa Su Yi Hattara October 12, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da HKI Kan Hare-Haren Da Take Kaiwa Kudancin Lebanon October 12, 2025 An Gudanar Da Taron ‘Farkawar Musulmi’ A Nan Tahren Inda Aka Tattauna Batun Falasdinu October 12, 2025 Amurka Da Masar Ne Zasu Jagoranci Taron Rattaba Hannu Tsakanin HKI Da Falasdin A Sharm Sheikh October 12, 2025 China Ta Sha Alwashin Maida Martani Kan Harajin Trump A Kanta Na 100% October 12, 2025 An Yi Girgizar Kasa Mai Daraja 5 A Ma’aunin Richter A Kasar Habasha October 12, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta October 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci