‘Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ce ta kama wasu da ake zargi da aikata laifuka, ta kwato bindigogi, da kuma kama sama da Naira miliyan 11 da ake zargin kudin fansa ne a cikin wannan lokaci.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Adekimi Ojo ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a Ilorin.

 

A cewarsa jami’an ‘yan sanda tare da hadin gwiwar kungiyoyin tsaro na cikin gida sun cafke wani kasurgumin mai garkuwa da mutane mai suna Idirisu Sariki a Okuta, karamar hukumar Baruten.

 

Ojo ya ce ana kyautata zaton Sariki na da alaka da sace-sacen mutane da dama a yankunan kan iyaka a jihar

 

Ya bayyana cewa, a yayin samamen jami’an tsaro sun kwato bindiga kirar AK-47, harsashi 13, da wata mota kirar Volkswagen Golf da aka ce ’yan ta’addan na amfani da su.

 

Ya yi nuni da cewa a yankin Share, karamar hukumar Ifelodun, an kama wasu mutane biyu Suleiman Jamiu da Mumini Mohammed a hannunsu da kudi Naira miliyan 11.3, wadanda ake zargin sun samu ne daga satar kudin fansa.

 

Ojo ya ce an kama wasu gungun mutane uku da suka hada da Mohammed Olaiya Dende da Mohammed Dende bisa laifin yin garkuwa da mutane a ranar 30 ga watan Mayu da 1 ga watan Yuni a Oro.

 

Ya ce wadanda ake zargin za su fuskanci tuhuma da suka hada da hada baki, garkuwa da mutane, da kuma kisan gilla, bayan harin da aka kai a wata cibiya ta cashewa da wata unguwar da ta yi sanadin mutuwar mutum daya tare da sace wasu mutane shida.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

Ya ce ya sayi layin wayar ne daga hannun wani Audu, ɗan kungiyar Vikings wanda ya tsere yanzu.

A wani lamari kuma, ‘yansanda sun kama wasu mutum huɗu da suka shiga gonar wani mutum a Lapai Gwari, inda suka saci kifi da darajar kuɗinsu ta kai Naira 750,000.

Babban wanda ake zargi, Hussaini Garba, ya amsa laifi tare da bayyana Ahmed Yusuf, Ibrahim Musa da Abdulazeez Bawa a matsayin mutanen da suke sayen kifin idan ya sato.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin