Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi
Published: 12th, July 2025 GMT
Ya kara da cewa, Asusun ya kuma gano fannonin aikin noman kasar da ya kamata a kara bunkasa su, wanda hakan ya sanya Asusun ya dauki wannan mataki.
Ya ci gaba da cewa, duba da irin amfanin gonar da manoma ke nomawa a kasar, musamman kananan manoma da kuma ribar da suke samu daga fannin, wani abu ne da Asusun ya dauka da ke da matukar muhimmanci, wanda kuma hakan ne ya kara bai wa Asusun kwarin guiwar shirin fara kaddamar da aikin.
Shi kuwa a nasa jawabin, Lanre Wilton-Wadell, mai taimaka wa Babban Sakataren a Asusun, ya yi bayani kan yadda za a gudanar da aikin.
Ya bayyana cewa, Asusun zai bayar da kashi 100 na Irin noma da takin zanani da kuma magungunan feshi, wanda za a gudanar a karkashin shirin aikin noma na kasa.
Ya ci gaba da cewa, bayan an girbe amfanin gonar, Asusun zai biya wadanda suka sarrafa amfanin gonar kashi 50 cikin 100 na jimillar kayan aikin noman da aka kashe kudade a kansu.
“Mun fito da wannan shiri ne, duba da cewa; ana samun rarrabuwa a kasuwannin kasar da kuma samar da dama ga masu sarrafa amfanin gona tare da kara habaka amfanin da manoman kasar ke nomawa,” in ji Lanre.
“Mun yi duba a kan hanyar da zamu tabbatar da mun hada manoma, yadda za su samu damar kai amfanin da suka noma zuwa kasuwanni kai tsaye tare kuma da samun damar ci gaba da sarrafa amfanin gonar da aka girbe,” a cewar Lanre.
Ya bayyana cewa, kashi 70 cikin 100 na manoman kasar, musamman kanannan manoma na fuskantar kalubalen ilimi, kan ingantaccen Irin noman da ya kamata su yi amfani da shi da kwarewar aikin noma.
Kazalika, ya sanar da cewa; su ma masu sarrafa amfanin gonar, ba sa iya samun ci gaba da samun amfanin da za su sarrafa, saboda ayyuakan masu tare manoman suna saye amfanin da suka noma a farashi mai sauki
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: sarrafa amfanin amfanin gonar
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin da ya sa muka gayyaci Sheikh Lawal Triumph – ’Yan sanda
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta bayyana dalilin da ya sa ta gayyaci malamin addini Sheikh Lawal Triumph.
A wata sanarwa da ta fitar, ’yan sanda sun ce sun sani cewa wasu daga cikin wa’azozin da Sheikh Triumph ke yi suna haddasa rashin jituwa a tsakanin al’ummar jihar.
Ya kamata mulkin Najeriya ya ci gaba da zama a hannun ’yan Kudu — Hannatu Musawa Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – ƊangoteRundunar ta ce kowa na da ’yancin faɗin albarkacin bakinsa, amma dole ne komai ya kasance bisa doka.
Saboda haka ne Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, ya gayyaci Sheikh Lawal Triumph don tattaunawa da jami’an gwamnati, shugabannin addini da na al’umma.
Manufar ita ce a nemi hanyar hana irin wannan rikici sake faruwa a nan gaba.
Rundunar ta kuma buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu su guji yin abubuwan da za su haifar da tashin hankali.
“Yana da muhimmanci a girmama ra’ayin juna da abin da mutane suka gaskata, kuma a tabbatar da cewa duk abin da mutum zai faɗa ko zai yi bai saɓa wa doka ba,” in ji rundunar.
Wannan lamari ya fara ne bayan wani wa’azi da Sheikh Lawal Triumph ya yi, wanda ya tayar da ƙura.
Ya faɗi haka ne a matsayin martani ga waɗanda suke musanta wani hadisi da ke cewa kwarkwata ƙazanta ce.
Wannan ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda wasu suka fara kiran a kashe Sheikh Lawal Triumph bisa zargin ya yi izgili ya Manzon Allah (S.A.W).
Rundunar ta kuma shawarci jama’a da su kai koken su ga hukumomin da suka dace, maimakon yaɗa saƙonni da za su iya tayar da hankali a shafukan sada zumunta.